Sabuwar ƙungiyar matasan arewacin Najeriya ta LND ƙarkashin jagorancin shugabanta kuma tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Ibrahim Shekarau, ta nemi a yi gyaran fuska ga sabon ƙudirin haraji mai cike da cece-kuce da shugaban ƙasar Bola Tinubu ya gabatarwa majalisar dokokin kasar.
Read Also:
- Rahoton ‘Yan Sanda ya Danganta Kashi 70% na Laifuka a Kano da Shaye-Shayen Miyagun Ƙwayoyi, Ya Gano Mutane 513 da ake Zargin Masu Safara Ne
- Pantami Ya Samu Karfin Gwiwa Yayin Da Jama’a Ke Taya Shi Murna a Lokacin Ziyarar Ayyuka a Gombe
- Ma’aikatar Tsaro ta yi Karin Bayani Kan Yarjejeniyar Yaki da Ta’addanci da Turkiyya, ta Karyata Zargin ‘Jihadi’
Ƙungiyar ta bayyana hakan ne a ranar Alhamis a Abuja a wajen gabatar da rahoton kwamitin kwararru da ta kafa domin yin nazari kan kudirin sake fasalin harajin da ya janyo cece-kuce a ƙasar.
Tun bayan gabatar da ƙudirin da shugaba Tinubu ya yi, na sake fasalin dokar haraji, ya haifar da zazzafar muhawara a fadin ƙasar, masamman masu fada a ji a yankin arewacin ƙasar da ke zargin zai haifar da koma baya ga yankin.












