Gwamnan Kano ya tura sabbin Kwamishinonin da ya Rantsar Zuwa Ma’aikatun da za suyi aiki

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya tura sabbin Kwamishinoni 7n da ya rantsar zuwa ma’aikatun da zasu kula masa dasu.

Kwamishinan shari’a na jihar kuma babban lauyan Gwamnati, Barista Haruna Isa Dederi ne ya rantsar da sabbin kwamishinonin 7, da sabbin manyan sakatarorin gwamnati guda 6 da aka daga likkafarsu, dama sauran masu baiwa gwamna shawara guda 13.

Sabbin Kwamishinonin dama ma’aikatun da aka tura su sune;

1. Alhaji Shehu Wada Sagagi – Ma’aikatar kasuwanci da zuba jari

2. Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya – Ma’aikatar yada Labarai

3. Dakta Dahir Muhammad Hashim – Ma’aikatar Muhalli

4. Abdulkadir Abdussalam -Ma’aikatar Raya Karkara

5. Dakta Isma’ila Aliyu Dan Maraya – Ma’aikatar Kudi

6. Dakta Gaddafi Sani Yakubu – Ma’aikatar Makamashi

7. Dakta Nura Iro Ma’aji – Ma’aikatar kula da kwangiloli da bibiyar ayyukan gwamnati

A karshe Gwamnan ya taya su murna tare da bukatar su rike gaskiya da amana, domin kiyaye rantsuwar da suka yi na yiwa jama’a aiki.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 18 hours 54 minutes 4 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 20 hours 35 minutes 29 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com