Home General Harin ISWAP ya hallaka sojojin Najeriya shida a jihar Borno

Harin ISWAP ya hallaka sojojin Najeriya shida a jihar Borno

Rahotannin daga jihar Borno dake Arewa maso gabashin Nijeriya na bayyana cewa Mayaƙa masu alaƙa da ƙungiyar ISWAP sun hallaka sojojin kasar shida yayin wani hari da suka kai kan sansaninsu, kamar yadda kamfanin yada labarai na AFP ya ruwaito

AFP ya ambato jami’an sojin Najeriya biyu na cewa maharan na ƙungiyar Islamic State West Africa Province (ISWAP) sun far wa sansanin da ke Sabon Gari a ƙaramar hukumar Damboa ranar Lahadi da tsakar dare.

Rahotonni sun ce sun cinna wa sansanin wuta tare da ababen hawan da ke cikinsa.

“An kashe mana sojoji shida a harin na Iswap da suka kai sansanin bayan zazzafar musayar wuta,” kamar yadda ɗaya daga cikin jami’an ya faɗa wa AFP.

Ɗaya jami’in ya ce jirgin sojin sama da aka aika daga binrin Maiduguri, mai nisan kilomita 100, shi ne ya kori maharan.

“Hare-hare ta sama ya kashe ‘yanbindigar da yawa, ya lalata motoci da makamansu,” in ji majiyar ba tare da bayar da yawan adadi ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp