Home General Gwamnan Kano ya tura sabbin Kwamishinonin da ya Rantsar Zuwa Ma’aikatun da...

Gwamnan Kano ya tura sabbin Kwamishinonin da ya Rantsar Zuwa Ma’aikatun da za suyi aiki

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya tura sabbin Kwamishinoni 7n da ya rantsar zuwa ma’aikatun da zasu kula masa dasu.

Kwamishinan shari’a na jihar kuma babban lauyan Gwamnati, Barista Haruna Isa Dederi ne ya rantsar da sabbin kwamishinonin 7, da sabbin manyan sakatarorin gwamnati guda 6 da aka daga likkafarsu, dama sauran masu baiwa gwamna shawara guda 13.

Sabbin Kwamishinonin dama ma’aikatun da aka tura su sune;

1. Alhaji Shehu Wada Sagagi – Ma’aikatar kasuwanci da zuba jari

2. Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya – Ma’aikatar yada Labarai

3. Dakta Dahir Muhammad Hashim – Ma’aikatar Muhalli

4. Abdulkadir Abdussalam -Ma’aikatar Raya Karkara

5. Dakta Isma’ila Aliyu Dan Maraya – Ma’aikatar Kudi

6. Dakta Gaddafi Sani Yakubu – Ma’aikatar Makamashi

7. Dakta Nura Iro Ma’aji – Ma’aikatar kula da kwangiloli da bibiyar ayyukan gwamnati

A karshe Gwamnan ya taya su murna tare da bukatar su rike gaskiya da amana, domin kiyaye rantsuwar da suka yi na yiwa jama’a aiki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp