Home General Gwamnan Kano ya tura sabbin Kwamishinonin da ya Rantsar Zuwa Ma’aikatun da...

Gwamnan Kano ya tura sabbin Kwamishinonin da ya Rantsar Zuwa Ma’aikatun da za suyi aiki

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya tura sabbin Kwamishinoni 7n da ya rantsar zuwa ma’aikatun da zasu kula masa dasu.

Kwamishinan shari’a na jihar kuma babban lauyan Gwamnati, Barista Haruna Isa Dederi ne ya rantsar da sabbin kwamishinonin 7, da sabbin manyan sakatarorin gwamnati guda 6 da aka daga likkafarsu, dama sauran masu baiwa gwamna shawara guda 13.

Sabbin Kwamishinonin dama ma’aikatun da aka tura su sune;

1. Alhaji Shehu Wada Sagagi – Ma’aikatar kasuwanci da zuba jari

2. Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya – Ma’aikatar yada Labarai

3. Dakta Dahir Muhammad Hashim – Ma’aikatar Muhalli

4. Abdulkadir Abdussalam -Ma’aikatar Raya Karkara

5. Dakta Isma’ila Aliyu Dan Maraya – Ma’aikatar Kudi

6. Dakta Gaddafi Sani Yakubu – Ma’aikatar Makamashi

7. Dakta Nura Iro Ma’aji – Ma’aikatar kula da kwangiloli da bibiyar ayyukan gwamnati

A karshe Gwamnan ya taya su murna tare da bukatar su rike gaskiya da amana, domin kiyaye rantsuwar da suka yi na yiwa jama’a aiki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp