Gwamnatin jihar Katsina dake arewa maso yammacin Nijeriya ta yabawa dakarun tsaron kasar da suka hadar da Sojojin Operation FANSAN YAMMA dakarun bataliya ta 17 na rundunar sojojin kasa, jami’an tsaro na sa kai da Vigilanti bisa nasarar tarwatsa maboyar ‘yan bindiga dake Kadoji, Matso-matso, Bagga, Dogon Marke da Takatsaba dake karamar hukumar Jibia.
Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da PRNigeria ta samu wadda kwamishinan tsaro da al’amuran cikin gida na jihar Dr. Nasir Muazu ya fitar aka kuma raba manema labarai a jihar.
Read Also:
Wannan dai na zuwa ne bayan wata gagarumar nasara da dakarun suka samu a wani hari da suka kai wa ‘yan bindigar a ranar 4 ga watan janairu, wanda ya kassarar ayyukan ta’addanci a kananan hukumomin Jibia, Batsari da Batagarawa duka a jihar katsina dake fama da matsalar rashin tsaro.
Harin hadin gwiwa ta sama da kasa ya samar da nasarar hallaka ‘yan bindiaga 80, yayin da masu yawa suka tsere da raunikan harbi a jukkunan, inda kuma jamián tsaron sauka tarwata maboyar da wasu cikin makamansu.
Sanarwa ta ce gwamnatin jihar Katsina ta nuna farin cikinta bisa wannan nasarar da aka samu bisa hadin kan jami’an da yunkurinsu na dawo da zaman lafiya a shiyyar arewa maso yamma dake fama da matsalar rashin tsaro.
PRNigeria Hausa
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 20 hours 44 minutes 3 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 22 hours 25 minutes 28 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com