Home General Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan Ta’adda 80 a jihar Katsina

Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan Ta’adda 80 a jihar Katsina

Gwamnatin jihar Katsina dake arewa maso yammacin Nijeriya ta yabawa dakarun tsaron kasar da suka hadar da Sojojin Operation FANSAN YAMMA dakarun bataliya ta 17 na rundunar sojojin kasa, jami’an tsaro na sa kai da Vigilanti bisa nasarar tarwatsa maboyar ‘yan bindiga dake Kadoji, Matso-matso, Bagga, Dogon Marke da Takatsaba dake karamar hukumar Jibia.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da PRNigeria ta samu wadda kwamishinan tsaro da al’amuran cikin gida na jihar Dr. Nasir Muazu ya fitar aka kuma raba manema labarai a jihar.

Wannan dai na zuwa ne bayan wata gagarumar nasara da dakarun suka samu a wani hari da suka kai wa ‘yan bindigar a ranar 4 ga watan janairu, wanda ya kassarar ayyukan ta’addanci a kananan hukumomin Jibia, Batsari da Batagarawa duka a jihar katsina dake fama da matsalar rashin tsaro.

Harin hadin gwiwa ta sama da kasa ya samar da nasarar hallaka ‘yan bindiaga 80, yayin da masu yawa suka tsere da raunikan harbi a jukkunan, inda kuma jamián tsaron sauka tarwata maboyar da wasu cikin makamansu.

Sanarwa ta ce gwamnatin jihar Katsina ta nuna farin cikinta bisa wannan nasarar da aka samu bisa hadin kan jami’an da yunkurinsu na dawo da zaman lafiya a shiyyar arewa maso yamma dake fama da matsalar rashin tsaro.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp