Home General Sojojin saman Nijeriya sun hallaka Dan Ta’adda Rusu da mayakansa a jihar...

Sojojin saman Nijeriya sun hallaka Dan Ta’adda Rusu da mayakansa a jihar Zamfara

Dakarun sojojin saman Nijeriya karkashin Operation Fansan Yamma sun sami nasarar hallaka dan bindigar nan Sani Rusu, a wani hari da ta kai kauye Bamamu dake karamar hukumar Tsafe a jihar Zamfara.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da Kodinatan cibiyar hadin gwiwa ta yada labaran dakarun Operation FANSAN YAMMA Abubakar Abdullahi ya aikewa PRNigeria a safiyar litinin 6 ga watan Janairu 2025.

Sanarwa ta ce yayin yarin saman da dakrun suka kai maboyar dan Ta’addan sun yi misayar wuta da mayakan dan bindiga inda suka sami nasarar tarwatsasu tare da hallaka Rusu dake addabar al’ummar yankin.

Haka kuma sanarwar ta kara da cewa a ranar 4 ga watan janairu dakarun Operation FANSAN YAMMA sun kai wani harin kwantan bauna, wanda ya basu nasarar dakile ayyukan taddanci a kwanar Jollo dake karamar hukumar Shinkafi a jihar Zamfara, in da suka sami nasarar hallaka ‘yan ta’adda tare da samun damar kwato tarin makamai da suka hadar da bindiga kirar AK47 bindiga kirar G3, hadi da zageyen alburusa masu tsayin 7.62mm na musamman da kuma wasu alburusan kirar NATO masu tsayin 7.62mm da babu hawa guda 3

Abubakar Abdullahi  ya kara da cewa dakarun Operation FANSAN YAMMA sun gudanar da wani hari ta sama a tsakanin Fakai da Kware a karamar hukumar ta shinkafi a ranar 30 ga watan disambar shekarar da ta gabata.

Wannan hari ya auku ne bayan samun bayanan sirri da ke nuna cewa ‘yan ta’addan na karkashin jagorancin dan ta’addan nan Bello Turji yayin da suke tsaka da ganawar sirri a yankin.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp