Home General Sojojin saman Nijeriya sun hallaka Dan Ta’adda Rusu da mayakansa a jihar...

Sojojin saman Nijeriya sun hallaka Dan Ta’adda Rusu da mayakansa a jihar Zamfara

Dakarun sojojin saman Nijeriya karkashin Operation Fansan Yamma sun sami nasarar hallaka dan bindigar nan Sani Rusu, a wani hari da ta kai kauye Bamamu dake karamar hukumar Tsafe a jihar Zamfara.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da Kodinatan cibiyar hadin gwiwa ta yada labaran dakarun Operation FANSAN YAMMA Abubakar Abdullahi ya aikewa PRNigeria a safiyar litinin 6 ga watan Janairu 2025.

Sanarwa ta ce yayin yarin saman da dakrun suka kai maboyar dan Ta’addan sun yi misayar wuta da mayakan dan bindiga inda suka sami nasarar tarwatsasu tare da hallaka Rusu dake addabar al’ummar yankin.

Haka kuma sanarwar ta kara da cewa a ranar 4 ga watan janairu dakarun Operation FANSAN YAMMA sun kai wani harin kwantan bauna, wanda ya basu nasarar dakile ayyukan taddanci a kwanar Jollo dake karamar hukumar Shinkafi a jihar Zamfara, in da suka sami nasarar hallaka ‘yan ta’adda tare da samun damar kwato tarin makamai da suka hadar da bindiga kirar AK47 bindiga kirar G3, hadi da zageyen alburusa masu tsayin 7.62mm na musamman da kuma wasu alburusan kirar NATO masu tsayin 7.62mm da babu hawa guda 3

Abubakar Abdullahi  ya kara da cewa dakarun Operation FANSAN YAMMA sun gudanar da wani hari ta sama a tsakanin Fakai da Kware a karamar hukumar ta shinkafi a ranar 30 ga watan disambar shekarar da ta gabata.

Wannan hari ya auku ne bayan samun bayanan sirri da ke nuna cewa ‘yan ta’addan na karkashin jagorancin dan ta’addan nan Bello Turji yayin da suke tsaka da ganawar sirri a yankin.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp