Home General Sojojin saman Nijeriya sun hallaka Dan Ta’adda Rusu da mayakansa a jihar...

Sojojin saman Nijeriya sun hallaka Dan Ta’adda Rusu da mayakansa a jihar Zamfara

Dakarun sojojin saman Nijeriya karkashin Operation Fansan Yamma sun sami nasarar hallaka dan bindigar nan Sani Rusu, a wani hari da ta kai kauye Bamamu dake karamar hukumar Tsafe a jihar Zamfara.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da Kodinatan cibiyar hadin gwiwa ta yada labaran dakarun Operation FANSAN YAMMA Abubakar Abdullahi ya aikewa PRNigeria a safiyar litinin 6 ga watan Janairu 2025.

Sanarwa ta ce yayin yarin saman da dakrun suka kai maboyar dan Ta’addan sun yi misayar wuta da mayakan dan bindiga inda suka sami nasarar tarwatsasu tare da hallaka Rusu dake addabar al’ummar yankin.

Haka kuma sanarwar ta kara da cewa a ranar 4 ga watan janairu dakarun Operation FANSAN YAMMA sun kai wani harin kwantan bauna, wanda ya basu nasarar dakile ayyukan taddanci a kwanar Jollo dake karamar hukumar Shinkafi a jihar Zamfara, in da suka sami nasarar hallaka ‘yan ta’adda tare da samun damar kwato tarin makamai da suka hadar da bindiga kirar AK47 bindiga kirar G3, hadi da zageyen alburusa masu tsayin 7.62mm na musamman da kuma wasu alburusan kirar NATO masu tsayin 7.62mm da babu hawa guda 3

Abubakar Abdullahi  ya kara da cewa dakarun Operation FANSAN YAMMA sun gudanar da wani hari ta sama a tsakanin Fakai da Kware a karamar hukumar ta shinkafi a ranar 30 ga watan disambar shekarar da ta gabata.

Wannan hari ya auku ne bayan samun bayanan sirri da ke nuna cewa ‘yan ta’addan na karkashin jagorancin dan ta’addan nan Bello Turji yayin da suke tsaka da ganawar sirri a yankin.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp