Gwamnan Kano ya mayar wa ‘yan APC martani kan zaɓen 2027

Gwamnan jihar Kano da ke arewacin Najeriya, Abba Kabir Yusuf, ya ce aikin hidimta wa Kano ne a gabansa yanzu “ba neman wa’adin mulki na biyu ba”.

Gwamnan na mayar da martani ne game da kalaman da tsohon shugaban jam’iyyar APC na Kano, Abdullahi Abbas, ya yi a farkon makon nan game da shirinsu na ƙwace mulkin jihar daga jam’iyyar NNPP a zaɓen 2027.

Kakakin gwamnatin jihar ta Kano, Sanusi Dawakin Tofa, ya faɗa cikin wata sanarwa cewa gwamnan ya yi martanin ne yayin taron tallafa wa mata a fadar gwamnatin jihar.

“Ba neman wa’adi na biyu ne ya fi damu na ba. Na fi damuwa da sauke nauyin alƙawurran da na ɗauka a wa’adin farko…kuma ina son mutanen Kano su yi min hukunci da ayyukana a ƙarshen mulkin,” a cewar gwamnan.

Jam’iyyar NNPP ta ƙwace mulkin Kano ne a zaɓen 2023 bayan APC ta yi wa’adin mulki biyu na shekara takwas ƙarƙashin Abdullahi Umar Ganduje.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1487 days 9 hours 39 minutes 16 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1469 days 11 hours 20 minutes 41 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com