Wasu rahotanni daga jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya sun ce ƴan ta’adda sun sake farmakar ayarin Sojin ƙasar da ke kan hanyarsu ta laluben gawarwakin manoma 40 da ISWAP ta hallaka a garin Dumba na yankin Baga da ke ƙaramar hukumar Kukawa a jihar.
Wasu majiyoyi daga yankin sun tabbatar da cewa mayaƙan ISWAP ne suka ƙaddamar da harin kuma har kawo yanzu babu cikakkun alƙaluman sojojin da aka rasa a wannan farmaki.
Wata majiya daga ɓangaren ƴan sa kan ta bayyana cewa tun da farko adadi mai yawa na Sojin Najeriya tare da ƴan sakai 54 ciki har da mafarauta ne suka shiga dajin don laluben gawarwakin sai dai har zuwa yanzu ɗan sa kai 1 ne tal ya dawo cikin Baga a galabaice.
Read Also:
A cewar bayanai sun ce da farko sojojin sun so daƙile harin ƴan ta’addan amma kuma yawan makaman da mayaƙan ke ɗauke da shi ya tilasta musu ja da baya.
Rahotanni sun ce babu tabbacin Soji nawa suka mutu ko kuma nawa suka jikkata haka zalika a ɓangaren mayaƙan na sa kai lura da cewa hatta mutum guda da ya dawo cikin gari baya cikin hayyacinsa da zai iya bayar da labarin abin da ya faru.
Sai dai wata majiya daga ɓangaren Sojin Najeriya ta ce tuni wasu daga cikin dakarun na ta suka dawo sansaninsu da ke Baga.
A cewar majiyoyin Sojin sun birne 15 daga cikin manoman da ƴan ta’addam suka kashe sai sun haɗu da farmaki a lokacin da suka kai tsakiyar hanya a ƙoƙarinsu na isa Dumba, amma sun ci gaba da tafiya bana kawar da barazanar ƴan ta’addan.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1464 days 1 hour 6 minutes 35 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1446 days 2 hours 48 minutes 0 second
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com