Hukumar rarraba lantarki ta Najeriya (TCN) ta sanar da cewa wasu mutane sun ɓarnata tare da sace kayan wuta da ke samar da lantarki ga wasu sassa na Abuja, babban birnin ƙasar.
Sanarwar da hukumar ta fitar a jiya Juma’a ta ce “an lalata layin wutar lantarkinta na 132kV da wayoyin ƙarƙashin ƙasa waɗanda ke kai lantarki zuwa cikin ƙwaryar Abuja da unguwannin da ke kewaye, lamarin da ya kawo katsewar lantarki”.
Lamarin dai ya jefa unguwannin Abuja da dama cikin duhu, tare da haifar da wahalahalu ga al’umma.
Sanarwar, wadda ta samu sa hannun jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Ndidi Mbah, ta ce wayoyin su ne ke kai lantarki ga cibiyoyin rarraba lantarki na kamfanin AEDC domin samar da lantarki ga al’umma.
“Lamarin wanda ya faru a kusa da Millenium Park da ke Abuja, ya shafi fiye da kashi 60 cikin ɗari na lantarkin da ake samar wa birnin,” in ji sanarwar.
Bayanin ya tabbatar da cewa maɓarnatan sun sace wayoyin lantarki da sauran kayan wuta da dama.
Unguwannin da abin ya shafa sun haɗa da Maitama, da Wuse, da Jabi, da Life Camp, da Asokoro, da Utako da kuma Mabushi.
Hukumar ta TCN ta ce ta tura jami’anta domin yin gyara a inda aka sace kayan.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1464 days 58 minutes 7 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1446 days 2 hours 39 minutes 32 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com