Home General Bama Bukatar yin siyasa da Kwankwaso – APC kano

Bama Bukatar yin siyasa da Kwankwaso – APC kano

Jam’iyyar APC ta jihar Kano ta ce kokarin shigowa APC Kwankwaso yake yi shi ne Dalilin sa ya Abdulmumin Jibrin Kofa ya fara kiraye-kirayen a sami sulhu tsakanin Kwankwaso da Ganduje.

“Maganar sulhu tsakanin Kwankwaso da Ganduje da Kofa yazo da ita yaudara ce, a siyasance ba ma buƙatar yin siyasa tare da Kwankwaso”.

Mai magana da yawun Jam’iyyar APC reshen jihar Kano Ahmad S Aruwa ne ya bayyana hakan yayin wata ganawa da ya yayi da Hikima Radio dake Kano.

” So suke so dawo APC don su kwace ta daga wajenmu, domin Kwankwaso ya saba yin hakan tun da ya yiwa Malam Ibrahim Shekarau Wanda ta dole sai da muka bar masa APC muka koma PDP, haka kuma ya sake yi mana a PDPn don haka mun gano wayon”. Inji Kakakin APC

Ya ce idan da gaske ke gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ne ya kamata ya dai-data Kwankwaso da Ganduje, amma ba Kofa ba.

” Idan ka lura da yadda Kofa ya tsayyano mukaman da Kwankwaso ya rike da wadanda Ganduje ya rike zaka gane shi (Kofa) ya yi kankanta ya ce zai sulhunta Kwankwaso da Ganduje”. A cewar Aruwa

Kakakin APC reshen jihar Kano ya ce su ba sa bukatar yin sulhu tsakanin Kwankwaso da Ganduje saboda a cewarsa daga karshe cewa za ayi a hade, kuma in an hade su za a cutar.

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito Dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Kiru da Bebeji Abdulmumin Jibrin Kofa a karshen makon da muke bankwana da shi , ya ce ya sama wajibi a sulhunta Ganduje da Kwankwaso saboda cigaban jihar Kano

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp