Home General Ana Fargabar Mutane Da Yawa Sun Mutu A Gobarar Tankar Mai A...

Ana Fargabar Mutane Da Yawa Sun Mutu A Gobarar Tankar Mai A Naija

Ana fargabar mutane da dama sun rasu wasu kuma sun jikkata, a yayin da suke kokarin dibar man fetur daga wata tankar mai da ta fadi a kwanar Dikko da ke babban titin Abuja zuwa Kaduna, a jihar Naija.

Rahotanni na cewa lamarin ya faru ne a yau Asabar, a lokacin da tankar da ke gudu ta fadi man ya zube, mutane suka je suna kwasar man sai motar ta yi bindiga wuta ta tashi.

Wutar ta kone mutane da dama da ke kwasar man yayin da wadanda suke nesa da ita kuwa suka ji rauni.

Kakakin gwamnan jihar Naija, Bologi Ibrahim, ya tabbatar wa da Emergency Digest faruwar lamarin, harma ya ce Gwamnan jihar Mohammed Bago, ya nuna alhininsa a kan Iftila’in.

A karshe ya umarci jami’an tsaro su tabbatar da tsaro a wajen, sannan sauran hukumomin gwamnatin jihar su yi abin da ya wajaba a kai.

Ko a watan Oktobar shekarar da ta wuce an sami makamancin wannan Iftila’i a garin Majiya da ke karamar hukumar Taura ta jihar Jigawa, inda sama da mutum 170 suka mutu, baya ga jikkatar sama da 50, a sakamakon fashewar tankar, lokacin da wasun su ke kwasar mai.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Abin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina
X whatsapp