Home General Ana Fargabar Mutane Da Yawa Sun Mutu A Gobarar Tankar Mai A...

Ana Fargabar Mutane Da Yawa Sun Mutu A Gobarar Tankar Mai A Naija

Ana fargabar mutane da dama sun rasu wasu kuma sun jikkata, a yayin da suke kokarin dibar man fetur daga wata tankar mai da ta fadi a kwanar Dikko da ke babban titin Abuja zuwa Kaduna, a jihar Naija.

Rahotanni na cewa lamarin ya faru ne a yau Asabar, a lokacin da tankar da ke gudu ta fadi man ya zube, mutane suka je suna kwasar man sai motar ta yi bindiga wuta ta tashi.

Wutar ta kone mutane da dama da ke kwasar man yayin da wadanda suke nesa da ita kuwa suka ji rauni.

Kakakin gwamnan jihar Naija, Bologi Ibrahim, ya tabbatar wa da Emergency Digest faruwar lamarin, harma ya ce Gwamnan jihar Mohammed Bago, ya nuna alhininsa a kan Iftila’in.

A karshe ya umarci jami’an tsaro su tabbatar da tsaro a wajen, sannan sauran hukumomin gwamnatin jihar su yi abin da ya wajaba a kai.

Ko a watan Oktobar shekarar da ta wuce an sami makamancin wannan Iftila’i a garin Majiya da ke karamar hukumar Taura ta jihar Jigawa, inda sama da mutum 170 suka mutu, baya ga jikkatar sama da 50, a sakamakon fashewar tankar, lokacin da wasun su ke kwasar mai.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp