Home General Mun kashe ƴanbindiga ciki har da ɗangidan Bello Turji – Sojoji

Mun kashe ƴanbindiga ciki har da ɗangidan Bello Turji – Sojoji

Dakarun Najeriya da suke aikin soji na musamman Fansan Yamma sun ce sun kashe ƴandinga da dama, ciki har da ɗan cikin Turji a wani samame da suka kai a sansanin ɗanbindigar.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da kakakin hedkwatar taron Najeriya, Edward Buba ya fitar, inda ya ce, “a ranar 17 ga Janairu, dakarun Fansan Yamma sun kutsa dazukan da ke yankin Shinkafi da Kagara da Fakai da Moriki da Maiwa da Chindo, inda suka kashe gomman ƴanbindiga, sannan suka kashe ɗan cikin Bello Turji a Fakai, inda yake ɓoyewa.”

Sanarwar ta ƙara da cewa sojojin sun samu ƙashe ƴanbindiga da dama, da ɓarnata ma’ajiyarsu, “sannan sun ceto wasu waɗanda Bello Turji ya yi garkuwa da su, bayan ya tsere.”

Sanarta ta ce sojojin sun kai wani samamen a sansanin wani ɗanbindigar mai suna Idi Mallam, “inda sojoji suka kashe ƴanbindiga 3, da kama mutum 3 da ake zargi da taimakon ƴanbindiga, tare da ƙwato wasu makamai da dabbobin da suka sace.”

A ƙarshe Buba ya ce sojojin za su cigaba da fatattarkar ƴanbindigar a ƙoƙarinsu na tabbatar da zaman lafiya a faɗin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp