Home General Najeriya ta buƙaci a samar da ƙasashen Isra’ila da Falasɗinu masu cin...

Najeriya ta buƙaci a samar da ƙasashen Isra’ila da Falasɗinu masu cin gashin kansu

Najeriya ta yi kira da a samar da ƙasashen Isra’ila da Falasɗinu masu cin gashin kansu, inda ta ce hakan ne zai wanzar da zaman lafiya a yankin.

Ƙasar ta bayyana haka ne a lokacin da take maraba da tsagaita wuta da aka yi a Gaza tsakanin Isra’ila da Hamas.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Najeriya, Kimiebi Ebienfa ne ya bayyana haka a zantawarsa da tashar Channels mai zaman kanta a Najeriya.

“Najeriya na kira ga dukkan ɓangarori su haɗa kai domin tabbatar da an cimma sauran matakan yarjejeniyar tsagaita wutar, sannan Najeriya na kira da a samar da ƙasashen biyu na Isra’ila da Falasɗinu masu cin gashin kansu a matsayin hanya ɗaya tilo da za a tabbatar da zaman lafiya a yankin,” in ji Ebienfa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp