Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta gudanar da bincike na musamman dangane musabbabin rikicin da ya faru a unguwar Rimin zakara, wanda yayi sanadiyyar rasa rayukan mutane uku da jikkata wasu da dama.
Kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ne ya bayyana hakan a zantawarsa da manema labarai kan rikicin da aka samu tsakanin jami’an tsaro da mutanan dake zaune a yankin.
Read Also:
Waiya ya kuma ce jami’ar Bayero ce ta nemi taimakon gwamnatin Kano dan a dawo mata da filayenta, wanda hakan yasa ta shiga tsakani kuma aka baiwa mutanan dake zaune a gurin wa’adin tashi kasancewar lokacin da aka basu ya riga ya ƙare.
Daga nan waiya yace ɓata gari ne suka shiga cikin lamarin domin tada zaune tsaye duk kuwa da jami’an tsaron da waɗancen mutanen suka gayyato gudun tada fitina.
Kwamishinan yaɗa labarai da ayyukan cikin gida Kwamared Waiya yace, lallai Gwamnatin Kano zata kafa kwamitin da zai gudanar da bincike kan wanda suka haddasa rikicin da yayi sanadiyyar rayukan mutane.
Idan za a iya tunawa a ranar litinin ne al’ummar unguwar Rimin zakara suka zargi ma’aikatar ƙasa ta Kano da rushe musu gidaje da hadin kan jami’ar Bayero, lamarin da ya jawo har jami’an tsaro suka kashe mutane 3 tare da jikka wasu 16 .
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1463 days 12 hours 2 minutes 25 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1445 days 13 hours 43 minutes 50 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com