Home General Majalisar dokokin jihar Kano ta amince da dokar kafa Jami’an tsaron jiha

Majalisar dokokin jihar Kano ta amince da dokar kafa Jami’an tsaron jiha

Majalisar jihar Kano
Majalisar jihar Kano

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta amince da dokar, kafa rundunar tsaro ta jiha domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Amincewar ta zo ne bayan wata zazzafar muhawara kan wasu sassa na dokar, wadda ta tanadi hana duk wani wanda ke cikin jam’iyyar siyasa jagorantar rundunar.

Shugaban masu rinjaye na majalisar, Honarabul Lawan Hussaini Dala, ya bayyana cewa an yi nazari sosai kan dokar don tabbatar da cewa tana da amfani ga kowane ɓangare na jihar.

dokar ta ba wa jami’an rundunar ikon ɗaukar makamai, cafke masu laifi da kuma hana aikata miyagun ayyuka, domin kara tabbatar da tsaron rayuka da kuma dukiyoyin al’umma a lungu da sako na jihar Kano.

A ƙarshe Dala ya tabbatar da cewa wanda zai jagoranci rundunar dole ne ya kasance ɗan jihar Kano kuma ba dan wata jam’iyyar siyasa ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp