Home Labarai Gwamnatin Kano ta magantu kan rikicin Rimin Zakara

Gwamnatin Kano ta magantu kan rikicin Rimin Zakara


Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta gudanar da bincike na musamman dangane musabbabin rikicin da ya faru a unguwar Rimin zakara, wanda yayi sanadiyyar rasa rayukan mutane uku da jikkata wasu da dama.

Kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ne ya bayyana hakan a zantawarsa da manema labarai kan rikicin da aka samu tsakanin jami’an tsaro da mutanan dake zaune a yankin.

Waiya ya kuma ce jami’ar Bayero ce ta nemi taimakon gwamnatin Kano dan a dawo mata da filayenta, wanda hakan yasa ta shiga tsakani kuma aka baiwa mutanan dake zaune a gurin wa’adin tashi kasancewar lokacin da aka basu ya riga ya ƙare.

Daga nan waiya yace ɓata gari ne suka shiga cikin lamarin domin tada zaune tsaye duk kuwa da jami’an tsaron da waɗancen mutanen suka gayyato gudun tada fitina.

Kwamishinan yaɗa labarai da ayyukan cikin gida Kwamared Waiya yace, lallai Gwamnatin Kano zata kafa kwamitin da zai gudanar da bincike kan wanda suka haddasa rikicin da yayi sanadiyyar rayukan mutane.

Idan za a iya tunawa a ranar litinin ne al’ummar unguwar Rimin zakara suka zargi ma’aikatar ƙasa ta Kano da rushe musu gidaje da hadin kan jami’ar Bayero, lamarin da ya jawo har jami’an tsaro suka kashe mutane 3 tare da jikka wasu 16 .

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp