Home Labarai Gwamnatin Kano ta magantu kan rikicin Rimin Zakara

Gwamnatin Kano ta magantu kan rikicin Rimin Zakara


Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta gudanar da bincike na musamman dangane musabbabin rikicin da ya faru a unguwar Rimin zakara, wanda yayi sanadiyyar rasa rayukan mutane uku da jikkata wasu da dama.

Kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ne ya bayyana hakan a zantawarsa da manema labarai kan rikicin da aka samu tsakanin jami’an tsaro da mutanan dake zaune a yankin.

Waiya ya kuma ce jami’ar Bayero ce ta nemi taimakon gwamnatin Kano dan a dawo mata da filayenta, wanda hakan yasa ta shiga tsakani kuma aka baiwa mutanan dake zaune a gurin wa’adin tashi kasancewar lokacin da aka basu ya riga ya ƙare.

Daga nan waiya yace ɓata gari ne suka shiga cikin lamarin domin tada zaune tsaye duk kuwa da jami’an tsaron da waɗancen mutanen suka gayyato gudun tada fitina.

Kwamishinan yaɗa labarai da ayyukan cikin gida Kwamared Waiya yace, lallai Gwamnatin Kano zata kafa kwamitin da zai gudanar da bincike kan wanda suka haddasa rikicin da yayi sanadiyyar rayukan mutane.

Idan za a iya tunawa a ranar litinin ne al’ummar unguwar Rimin zakara suka zargi ma’aikatar ƙasa ta Kano da rushe musu gidaje da hadin kan jami’ar Bayero, lamarin da ya jawo har jami’an tsaro suka kashe mutane 3 tare da jikka wasu 16 .

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp