Home Labarai Gwamnatin Kano ta magantu kan rikicin Rimin Zakara

Gwamnatin Kano ta magantu kan rikicin Rimin Zakara


Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta gudanar da bincike na musamman dangane musabbabin rikicin da ya faru a unguwar Rimin zakara, wanda yayi sanadiyyar rasa rayukan mutane uku da jikkata wasu da dama.

Kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ne ya bayyana hakan a zantawarsa da manema labarai kan rikicin da aka samu tsakanin jami’an tsaro da mutanan dake zaune a yankin.

Waiya ya kuma ce jami’ar Bayero ce ta nemi taimakon gwamnatin Kano dan a dawo mata da filayenta, wanda hakan yasa ta shiga tsakani kuma aka baiwa mutanan dake zaune a gurin wa’adin tashi kasancewar lokacin da aka basu ya riga ya ƙare.

Daga nan waiya yace ɓata gari ne suka shiga cikin lamarin domin tada zaune tsaye duk kuwa da jami’an tsaron da waɗancen mutanen suka gayyato gudun tada fitina.

Kwamishinan yaɗa labarai da ayyukan cikin gida Kwamared Waiya yace, lallai Gwamnatin Kano zata kafa kwamitin da zai gudanar da bincike kan wanda suka haddasa rikicin da yayi sanadiyyar rayukan mutane.

Idan za a iya tunawa a ranar litinin ne al’ummar unguwar Rimin zakara suka zargi ma’aikatar ƙasa ta Kano da rushe musu gidaje da hadin kan jami’ar Bayero, lamarin da ya jawo har jami’an tsaro suka kashe mutane 3 tare da jikka wasu 16 .

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp