Home General Gwamnatin Kano Ta Sanar Da Ranar Hutun Makarantun Firamare Da Sakandiren Jihar

Gwamnatin Kano Ta Sanar Da Ranar Hutun Makarantun Firamare Da Sakandiren Jihar

Gwamnatin jihar Kano ta amince da ranar juma’a 28 ga watan Fabrairun 2025, a matsayin ranar hutun Zango karatu na biyu ga makarantun firamare da sakandire dake faɗin jihar.

Ma’aikatar ilimi ta jihar Kano ce ta sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da daraktan wayar da kan al’umma na ma’aikatar Balarabe Abdullahi Kiru ya rabawa manema labarai, inda ya ce hutun ya shafi makarantu masu zaman kansu da kuma na gwamnati.

Sanarwar ta ce daliban makarantun firamare da sakandire na kwana za su koma Makarantunsu a ranar lahadi 06 ga watan Afirilun 2025, a yayin da su kuma na makarantun jeka ka dawo za su koma Makarantar a ranar litinin 07 ga watan Afirilu, 2025.

Kwamishinan ilimi na jihar Kano Dakta Ali Haruna Makoda, ya buƙaci iyayen yaran da su tabbatar da cewa ‘ya’yansu sun koma Makarantar a ranakun da aka sanya.

A ƙarshe sanarwar ta gargaɗi dukkan makarantu masu zaman kansu da su tabbatar da bin ƙa’idar da aka gindaya ko kuma su fuskanci hukunci.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp