Home General Gwamnatin Kano Ta Sanar Da Ranar Hutun Makarantun Firamare Da Sakandiren Jihar

Gwamnatin Kano Ta Sanar Da Ranar Hutun Makarantun Firamare Da Sakandiren Jihar

Gwamnatin jihar Kano ta amince da ranar juma’a 28 ga watan Fabrairun 2025, a matsayin ranar hutun Zango karatu na biyu ga makarantun firamare da sakandire dake faɗin jihar.

Ma’aikatar ilimi ta jihar Kano ce ta sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da daraktan wayar da kan al’umma na ma’aikatar Balarabe Abdullahi Kiru ya rabawa manema labarai, inda ya ce hutun ya shafi makarantu masu zaman kansu da kuma na gwamnati.

Sanarwar ta ce daliban makarantun firamare da sakandire na kwana za su koma Makarantunsu a ranar lahadi 06 ga watan Afirilun 2025, a yayin da su kuma na makarantun jeka ka dawo za su koma Makarantar a ranar litinin 07 ga watan Afirilu, 2025.

Kwamishinan ilimi na jihar Kano Dakta Ali Haruna Makoda, ya buƙaci iyayen yaran da su tabbatar da cewa ‘ya’yansu sun koma Makarantar a ranakun da aka sanya.

A ƙarshe sanarwar ta gargaɗi dukkan makarantu masu zaman kansu da su tabbatar da bin ƙa’idar da aka gindaya ko kuma su fuskanci hukunci.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp