Gwamnatin Kano Ta Sanar Da Ranar Hutun Makarantun Firamare Da Sakandiren Jihar

Gwamnatin jihar Kano ta amince da ranar juma’a 28 ga watan Fabrairun 2025, a matsayin ranar hutun Zango karatu na biyu ga makarantun firamare da sakandire dake faɗin jihar.

Ma’aikatar ilimi ta jihar Kano ce ta sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da daraktan wayar da kan al’umma na ma’aikatar Balarabe Abdullahi Kiru ya rabawa manema labarai, inda ya ce hutun ya shafi makarantu masu zaman kansu da kuma na gwamnati.

Sanarwar ta ce daliban makarantun firamare da sakandire na kwana za su koma Makarantunsu a ranar lahadi 06 ga watan Afirilun 2025, a yayin da su kuma na makarantun jeka ka dawo za su koma Makarantar a ranar litinin 07 ga watan Afirilu, 2025.

Kwamishinan ilimi na jihar Kano Dakta Ali Haruna Makoda, ya buƙaci iyayen yaran da su tabbatar da cewa ‘ya’yansu sun koma Makarantar a ranakun da aka sanya.

A ƙarshe sanarwar ta gargaɗi dukkan makarantu masu zaman kansu da su tabbatar da bin ƙa’idar da aka gindaya ko kuma su fuskanci hukunci.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1463 days 6 hours 30 minutes 53 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1445 days 8 hours 12 minutes 18 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com