Gwamman jihar kano engr abba kabir yusuf, Ya amince da kafa kwamitin da zai bincike dalilin da yasa aka yankewa wasu daga cikin Ma’aikatan jihar kano a wannan wata da Muke ciki.
Cikin wata sanarwa da darktan Yada Labarai na Gwamann Sunusi bature dawakin Tofa ya fitar aka rabawa Manema Labarai yace, gwamman ya nuna damuwarsa da samun Labarin wanda hakan yasa ya kafa kwamitin.
Sakataren gwamnantin jihar kano Ahaji Umar Faruk Ibrahim shine ya kaddamar yan kwamitin a ofishinsa a yau alhamis.
Read Also:
An baiwa kwamitin wa’adin kwanaki 7 domin gabatar da rahotonsa akan wanann matsala da aka samu domin ya gano ko tangardar na’ura ce ko kuma zagon kasa ne da ake kokarin yiwa gwamnantin jihar kano domin Daukar mataki
Kwamitin zai kasance karkashin. Hon. Abdulkadir Abdussalam – Chairman wanda shine kwamishinan raya karkara da raya birane.
Dr. Bashir Abdu Muzakkari
Dr. Aliyu Isa Aliyu
4. Dr. Hamisu Sadi Ali
6. Aliyu Muhammad Sani
7. Ummulkulthum Ladan Kailani
Mikiya Hausa Times ta rawaito cewa wasu Ma’aikatan jihar kano ne suka koka da cewa an yanke musu albashi na wannan wata da muke ciki kamar yadda rahotanni suka bayyana.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 22 hours 28 minutes 39 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1445 days 10 minutes 4 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com