Home General Gwamnatin Jihar Kano ta bukaci Tinubu ya dauke Aminu Ado daga gidan...

Gwamnatin Jihar Kano ta bukaci Tinubu ya dauke Aminu Ado daga gidan Nassarawa

Gwamnatin jihar kano ta bukaci shugaban kasa Bola Tinubu da ya dauke sarkin kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero daga jihar kano domin samar da masalaha a jihar, la’akari da yadda wasu ke amfani dawannan damar wajen neman tayar da husuma a fadin jihar .

Mataimakin gwamnan jihar kano kwamrat Aminu Abdussalam Gwarzo ne ya bayyana hakan, inda yace zaunar da sarkin kano na 15 a gidan sarkin na Nassarawa anyi shi da wata niya domin hana gwamnatin kano ta zauna lafiya da kuma kin yiwa al’ummar jihar abin da ya dace.

Freedom Radio ta rawaito kwamrat Aminu Abdussalam Gwarzo yace zanga-zanga da al’umma su ka fito a wannan satin, al’umma suna da hakkin fitowa domin nuna goyon bayan su kan abin da suke so.

Haka kuma suna da damar su nemi a cire sarkin kano na sha biyar daga gidan Nasarawa amma aka turo jami’an tsaro suka hana su tare da kama wasu daga cikinsu.

Gwarzo ya kuma ce suna kira ga shugaban kasa da ya gaggauta dauke sarkin kano na sha biyar daga cikin jihar Kano domin barin al’umma su zauna lafiya.

Gwamnatin kano ta ce yadda doka ta kawo tsohon sarkin haka doka ce ta kawo sabon sarkin dan haka abar doka ta yi aiki

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp