Home General Badakala- Gwamnan Kano ya dakatar da mukaddashin Shugaban Ma’aikatan Jihar

Badakala- Gwamnan Kano ya dakatar da mukaddashin Shugaban Ma’aikatan Jihar

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya dakatar da mai rikon mukamin shugaban ma’aikata kuma babban sakatare na Establishment Salisu Mustapha, bisa zargin zarge-zargen da ake yi na yanke albashin ma’aikatan gwamnatin Kano.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a ranar Alhamis, ya tabbatar da cewa an kuma umurci Salisu Mustapha da ya ajiye mukaminsa na babban Sakatare na Establishment, a karkashin ofishin shugaban ma’aikata, don ba da damar gudanar da bincike ba tare da tangarda ba.

Domin tabbatar da ci gaba da gudanar da harkokin mulki, gwamnan ya amince da nadin Malam Umar Muhammad Jalo, Babban Sakatare na REPA, a matsayin sabon shugaban ma’aikata na riko, har sai an kammala binciken da ake yi.

Gwamna Yusuf ya sake jaddada matsayinsa na kin amincewa da almundahanar kudi, yana mai gargadin cewa duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci mummunan hukunci.

Kwamitin binciken da Abdulkadir Abdussalam ke jagoranta da aka kaddamar a yau, an ba shi wa’adin kwanaki bakwai don gano inda matsalar ta ke tare da gabatar da sakamakon binciken.

A farkon wannan watan ne aka nada Salisu Mustapha a matsayin shugaban ma’aikata na riko, biyo bayan hutun jinya da aka baiwa babban shugaban ma’aikatan, Abdullahi Musa, wanda yanzu haka yake jinya a kasar Indiya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp