Home General Na Sami tarbiyya bazan iya cin zarafin Mata ba – Akpabio

Na Sami tarbiyya bazan iya cin zarafin Mata ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya Godswill Akpabio ya musanta zargin cin zarafi ta hanyar lalata da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta yi a kansa.

Ya musanta zargin ne a ranar Laraba bayan majalisar ta koma aiki daga gajeren hutun da ta tafi.

Sanata Akpabio ya nuna rashin jin daɗinsa game da abubuwan da ke yawo a shafukan sada zumunta kan zargin da ake masa inda ya yi watsi da shi baki ɗaya.

“Ban taɓa cin zarafin wata mace ba. Na samu tarbiyya daga mahaifiyata, kuma ina girmama mata. An taɓa ba ni lambar yabo ta gwamnan da ya fi kyautata wa mata a Nijeriya,” kamar yadda Sanata Akpabio ya bayyana.

Bayan nan ne sai Sanata Natasha ta miƙe tsaye ta gabatar da korafi a kansa a hukumance a gaban majalisar bisa zarge-zargen da take masa.

A yayin da take gabatar da ƙorafin, ta zargi Akpabio da cin zarafi ta hanyar lalata da amfani da ƙarfin iko ba bisa ƙa’ida ba da kuma tauye mata haƙƙinta na gudanar da ayyukan majalisa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp