WHO zata ta bawa Nijeriya maganin cutar kuturta

Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO ta ce za ta aika magungunan cutar kuturta zuwa Najeriya, bayan magance jinkirin da aka samu, lamarin da ya sa dubban masu ɗauke da cutar a ƙasar suka shafe shekara guda ba tare da samun magani ba.

Najeriya – wadda ta bayar da rahoton samun dubban sabbin waɗanda suka kamu da cutar – ta kasance ba ta da maganin cutar saboda riƙe magungunan da aka yi bayan ɓullo da sabbin dokokin gwaji.

Kuturta cuta ce da ake iya maganinta da magunguna daban-daban. Kuma kasancewa Najeriya ta shafe tsawon shekara guda ba tare da maganin ba, jikin wasu masu ɗauke da cutar ya tsananta, sakamakon cutar da ke yanke yatsun hannu da ƙafa tare da shafar ƙwaƙwalwa.

Da dama cikin marasa lafiyar an sallame su daga asibiti domin komawa gida, wani abu da ke ƙara hatsarin yaɗa cutar.

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce ta buƙaci Najeriya ta ɗage sabbin dokokin gwajin magungunan, inda yanzu kuma ake sa ran rukunin farko na magungunan su isa ƙasar ranar Asabar daga Indiya.

Cikin fiye da shekara 40 cutar kuturta ta ragu matuƙa a faɗin duniya. Amma Najeriya na bayar da rahoton samun ƙaruwar masu kamuwa da cutar fiye da 1,000 a shekarar da ta gabata.

Akwai fiye da mutum 10,000 da ke kamuwa da cutar cikin shekara guda a ƙasashen Brazil da Indiya da kuma Indonesia.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1463 days 30 minutes 19 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1445 days 2 hours 11 minutes 44 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com