Home General WHO zata ta bawa Nijeriya maganin cutar kuturta

WHO zata ta bawa Nijeriya maganin cutar kuturta

Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO ta ce za ta aika magungunan cutar kuturta zuwa Najeriya, bayan magance jinkirin da aka samu, lamarin da ya sa dubban masu ɗauke da cutar a ƙasar suka shafe shekara guda ba tare da samun magani ba.

Najeriya – wadda ta bayar da rahoton samun dubban sabbin waɗanda suka kamu da cutar – ta kasance ba ta da maganin cutar saboda riƙe magungunan da aka yi bayan ɓullo da sabbin dokokin gwaji.

Kuturta cuta ce da ake iya maganinta da magunguna daban-daban. Kuma kasancewa Najeriya ta shafe tsawon shekara guda ba tare da maganin ba, jikin wasu masu ɗauke da cutar ya tsananta, sakamakon cutar da ke yanke yatsun hannu da ƙafa tare da shafar ƙwaƙwalwa.

Da dama cikin marasa lafiyar an sallame su daga asibiti domin komawa gida, wani abu da ke ƙara hatsarin yaɗa cutar.

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce ta buƙaci Najeriya ta ɗage sabbin dokokin gwajin magungunan, inda yanzu kuma ake sa ran rukunin farko na magungunan su isa ƙasar ranar Asabar daga Indiya.

Cikin fiye da shekara 40 cutar kuturta ta ragu matuƙa a faɗin duniya. Amma Najeriya na bayar da rahoton samun ƙaruwar masu kamuwa da cutar fiye da 1,000 a shekarar da ta gabata.

Akwai fiye da mutum 10,000 da ke kamuwa da cutar cikin shekara guda a ƙasashen Brazil da Indiya da kuma Indonesia.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp