Home General Tinubu ya bawa Jega Mukami

Tinubu ya bawa Jega Mukami

Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu ya nada Farfesa Attahiru Jega a matsayin mai ba shi shawara kuma babban jami’in kwamitin bunkasa kiwon dabbobi na kasar.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa Bayo Onanuga ya sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai.

Attahiru Jega mai shekaru 68 ya rike mukamin shugaban hukumar zaben Nijeriya daga shekarar 2010 zuwa 2015.

Kafin mukamin da Shugaba Tinubu ya ba shi a yammacin Jumma’ar nan, shi ne ya jagoranci kwamitin gyaran kiwon dabbobi da ya bai wa gwamnatin Tinubu shawarar kafa ma’aikata ta musamman don bunkasa kiwon dabbobi wacce yanzu ke da minista.

Sanarwar ta ce ana sa rana Farfesa Attahiru Jega zai yi amfani da gogewar da wajen habbaka harkokin kiwon dabbobi a Nigeria kamar yadda suka bayar da samar da ma’aikata sukutum da guda.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp