Home General NMDPRA ta sake bayar da lasisin buɗe sabbin matatun man fetur a...

NMDPRA ta sake bayar da lasisin buɗe sabbin matatun man fetur a Najeriya.

Hukumar Kula da Albarkatun Mai Na Ƙasa (NMDPRA) ta bayar da lasisin buɗe sabbin matatun man fetur a Najeriya.

Hukumar ta ce ta ba wasu kamfanoni guda uku lasisin ne domin buɗe matatun a jihohin Abia da Delta da Edo.

Shafin intanet na tashar Channels ne ya kalato labarin daga shafin X na NMDPRA, inda ya ƙara da cewa za a buɗe Matatar Eghudu wadda za ta iya tace ganga 100,000 a kullum a jihar Edo.

Za kuma da Matatar MB wadda za ta riƙa tace ganga 30,000 a kullum a jihar Delta, sai Matatar HIS wadda ita kuma za ta riƙa tace ganga 10,000 a kullum a jihar Abia, kamar yadda sanarwar, wadda shugaban hukumar, Farouk Ahmed ya bayyana ta nuna.

Idan aka kammala su, matatun guda uku za su riƙa tace ganga 140,000 ke nan a kullum.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp