Home General WHO zata ta bawa Nijeriya maganin cutar kuturta

WHO zata ta bawa Nijeriya maganin cutar kuturta

Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO ta ce za ta aika magungunan cutar kuturta zuwa Najeriya, bayan magance jinkirin da aka samu, lamarin da ya sa dubban masu ɗauke da cutar a ƙasar suka shafe shekara guda ba tare da samun magani ba.

Najeriya – wadda ta bayar da rahoton samun dubban sabbin waɗanda suka kamu da cutar – ta kasance ba ta da maganin cutar saboda riƙe magungunan da aka yi bayan ɓullo da sabbin dokokin gwaji.

Kuturta cuta ce da ake iya maganinta da magunguna daban-daban. Kuma kasancewa Najeriya ta shafe tsawon shekara guda ba tare da maganin ba, jikin wasu masu ɗauke da cutar ya tsananta, sakamakon cutar da ke yanke yatsun hannu da ƙafa tare da shafar ƙwaƙwalwa.

Da dama cikin marasa lafiyar an sallame su daga asibiti domin komawa gida, wani abu da ke ƙara hatsarin yaɗa cutar.

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce ta buƙaci Najeriya ta ɗage sabbin dokokin gwajin magungunan, inda yanzu kuma ake sa ran rukunin farko na magungunan su isa ƙasar ranar Asabar daga Indiya.

Cikin fiye da shekara 40 cutar kuturta ta ragu matuƙa a faɗin duniya. Amma Najeriya na bayar da rahoton samun ƙaruwar masu kamuwa da cutar fiye da 1,000 a shekarar da ta gabata.

Akwai fiye da mutum 10,000 da ke kamuwa da cutar cikin shekara guda a ƙasashen Brazil da Indiya da kuma Indonesia.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp