Majalisar wakilan Nijeriya ta ce a yau zata fara tsefe rahoton kwamitin sauraron ra’ayin jama’a kan ƙudirin dokar haraji.
Kakakin Majalisar, Hon. Tajudeen Abbas ne ya bayyana haka a zaman majalisar na ranar Laraba.
Hon Tajudeen ya ce majalisar za ta ɗauki tsawon wunin yau, Alhamis tana nazari da muhawara kan sassan ƙudirin dokar daban-daban.
Kakakin majalisar ya kuma yi kira ga duka mambobin majalisar su halarci zaman domin bayar da tasu gundunmawa kan rahoton kwamitin sauraron ra’ayin jama’ar.
Tuni dai kwamitin sauraron ra’ayin jama’ar – ƙarƙashin jagorancin shugaban kwamitin kuɗi na majalisar, Hon James Abiodun Faleke – ya kammala sauraron jin ra’ayin jama’a inda ya miƙa rahoton nasa a gaban majalisar a ranar Talata
A watan Oktoban bara ne shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya gabatar da ƙudurori huɗu da suka shafi haraji a gaban majalisun dokokin ƙasar, domin amincewa da su.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 16 hours 14 minutes 49 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 17 hours 56 minutes 14 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com