Home General PSC ta amince da Nadin CP Ibrahim Adamu Bakori matsayin kwamishinan ‘yan...

PSC ta amince da Nadin CP Ibrahim Adamu Bakori matsayin kwamishinan ‘yan sandan Jihar Kano

Hukumar kula da aikin Ƴansanda ta Najeriya (PSC), ta amince da naɗa CP Ibrahim Adamu Bakori, a matsayin sabon kwamishinan ƴansandan jihar Kano.

Shugaban hukumar, DIG Hashimu Argungu mai ritaya ne ya tabbatar da naɗin inda ya nemi sabon kwamishinan da ya tabbatar da an samu zaman lafiya mai ɗorewa a jihar, ta hanyar tunkarar ƙalubalen da ke gabansa wajen tabbatar da an daƙile ƙaruwar aikata laifuka a jihar mai yawan jama’a.

CP Bakori dai zai maye gurbin CP Salman Garba Dogo ne biyo bayan samun ƙarin girma zuwa mataimakin babban sifeto na ƙasa (AIG), kamar yadda sashen Hausa na BBC ya rawaito.

Kafiin naɗin nasa, CP Bakori ya kasance kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen binciken kisan kai (Homicide) a shelkwatar ƴansandan ƙasar da ke Abuja.

Jihar Kano dai na fama da matsalolin dabanci da ƙwacen waya da sace-sace, baya ga na baya-bayan nan wato rikicin masarautar Kano da ya janyo al’umma suka sauya tunaninsu kan rundunar ƴansandan jihar.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp