Home General PSC ta amince da Nadin CP Ibrahim Adamu Bakori matsayin kwamishinan ‘yan...

PSC ta amince da Nadin CP Ibrahim Adamu Bakori matsayin kwamishinan ‘yan sandan Jihar Kano

Hukumar kula da aikin Ƴansanda ta Najeriya (PSC), ta amince da naɗa CP Ibrahim Adamu Bakori, a matsayin sabon kwamishinan ƴansandan jihar Kano.

Shugaban hukumar, DIG Hashimu Argungu mai ritaya ne ya tabbatar da naɗin inda ya nemi sabon kwamishinan da ya tabbatar da an samu zaman lafiya mai ɗorewa a jihar, ta hanyar tunkarar ƙalubalen da ke gabansa wajen tabbatar da an daƙile ƙaruwar aikata laifuka a jihar mai yawan jama’a.

CP Bakori dai zai maye gurbin CP Salman Garba Dogo ne biyo bayan samun ƙarin girma zuwa mataimakin babban sifeto na ƙasa (AIG), kamar yadda sashen Hausa na BBC ya rawaito.

Kafiin naɗin nasa, CP Bakori ya kasance kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen binciken kisan kai (Homicide) a shelkwatar ƴansandan ƙasar da ke Abuja.

Jihar Kano dai na fama da matsalolin dabanci da ƙwacen waya da sace-sace, baya ga na baya-bayan nan wato rikicin masarautar Kano da ya janyo al’umma suka sauya tunaninsu kan rundunar ƴansandan jihar.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp