Home General Dalilin da ya sa muka hana Fubara shiga Majalisa

Dalilin da ya sa muka hana Fubara shiga Majalisa

Jami’an tsaron da ke gadin harabar majalisar dokokin jihar Rivers sun ƙulle ƙofar majalisar tare da hana gwamnan jihar Siminalayi Fubara shiga zauren majalisar.

Cikin wani bidiyo da sakataren yaɗa labaran gwamnan ya wallafa shafinsa na Facebook ya ce Fubara ya je majalisar ne domin gabatar da kasafin kuɗin jihar na 2025.

Rahotonni daga birnin Fatakwal sun ce tarin jami’an tsaron da aka jibge a harabar sun rufe ƙofar shiga majalisar a lokacin da gwamnan ya hallara tare da tawagarsa domin gabatar da kasafin.

Bayanai sun ambato jami’an tsaron na cewa sun yi hakan ne saboda ba a sanar da su labarin zuwan gwamnan a hukumance ba.

To sai dai Gwamna Fubara ya ce tuni ya aike wa kakakin majalisar, Martins Amaewhule wasikar sanar da shi zuwansa, kuma ya yi ƙoƙarin kiransa a waya tun ranar Talata.

A makonnin da suka gabata ne dai Kotun Ƙolin ƙasar ta yanke hukunci hana CBN bai wa jihar kason kuɗaɗenta daga tarayya saboda rashin gabatar da kasafin kuɗi a gaban halastacciyar majalisar dokokin jihar.

Haka kuma kotun ta yanke hukuncin maido da ƴanmajalisar jihar 27 da suka sauya sheƙa zuwa APC, tare da soke zaɓen ƙananan hukumomin jihar.

To sai dai a ranar 28 ga watan Fabrairu, Fubara ya sanar da yin aiki da hukuncin kotun tare da umartar hukumar zaɓen jihar ta shirya sabon zaɓen ƙananan hukumomin.

Tuni dai hukumar ta saka ranar 9 ga watan Agustan 2025 domin gudanar da sabon zaɓe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp