Home General Tinubu ya magantu kan rikicin jihar Rivers

Tinubu ya magantu kan rikicin jihar Rivers

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya buƙaci jagororin yankin Naija Delta su shawarci gwamnan jihar Rivers Siminalayi Fubara ya yi biyayya ga hukuncin Kotun Ƙolin ƙasar kan rikicin siyasar jihar.

Yayin da yake jawabi da masu ruwa da tsaki na yankin kudu maso kudancin ƙasar, ƙarƙashin ƙungiyar ci gaban yankin Naija Delta a fadarsa da ke Villa ranar Talata, shugaba Tinubu ya ce ya ɗora alhakin samar da zaman lafiyar jihar River a wuyan jagororin ƙungiyar.

Shugaba Tinubu ya buƙaci sadaukarwar jagororin yankin wajen ganin jihar ta yi aiki da kundin tarin mulkin ƙasar, ta hanyar yin biyayya ga dokokin ƙasar don samun zaman lafiya da kwanciyar hankali.

”Mutunta ɓangaren shari’a muhimmin ɓangare ne a tsarin dimokraɗiyya,” kamar yadda shugaban ƙasar ya ya bayyana, cikin sanarwar da kakakinsa, Bayo Onanuga ya fitar.

Ya ƙara da cewa ”Wannan ƙasa ce da ake amfani da dokokin na shari’a, inda babu waɗannan dokoki, da ban zama shugaban ƙasa ba, na yi imani da tsarin dimokraɗiyyarmu, muna da fata mai kyau. Ɗan’adam kan yi kuskure, amma idan kotu ta yanke hukunci to zance ya ƙare”, a cewar shugaban ƙasar.

“Don haka ina roƙonku, ku koma gida ku taimaka a yi amfani da hukunci kotu cikin ƙanƙanin lokaci, na ɗora alhakin a kanku, ku taimaka ku shiga tsakani a sirrance da kuma zahiri ku shawarci gwamna, a rungumi hanyar zaman lafiya da kwanciyar hankali”, a cewar Shugaba Tinubu.

A kwanakin baya ne dai kotun ƙolin Najeriya ta yanke hukuncin soke zaɓen ƙananan hukumomin jihar tare da mayar da ƴanmajalisar jihar 27 da suka sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC ma hamayya a jihar, wani abu da bai yi wa gwamnan jihar daɗi ba.

Kodayake cikin wani jawabi da ya yi wa al’ummar jihar bayan yanke hukuncin gwamnan ya ce gwamnatin jihar za ta bai wa hukumar zaɓen jihar goyon bayan sake shirya wani zaɓen ƙananan hukumomin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp