Home General Za a yi wa ɗalibai riga-kafin Diphtheria a Legas bayan mutuwar wani...

Za a yi wa ɗalibai riga-kafin Diphtheria a Legas bayan mutuwar wani ɗalibi

Jam’ian kiwon lafiya a jihar Legas sun ƙaddamar da shirin riga-kafi na gaggawa bayan samun ɓarkewar cutar Diphtheria da ya yi sanadiyyar mutuwar wani ɗalibi mai shekara 12 a wata makarantar sakandare.

Aƙalla mutane 34 suka yi mu’amala da shi kuma ana sanya musu ido, yayin da ɗalibai 14 daga makarantar kwanan mai suna King’s College suka nuna alamu kuma aka tabbatar da cewa 12 daga cikinsu na da cutar, inda tuni aka fara ba su magani.

A cewar ma’aikatar lafiya ta jihar Legas, yaron ya fara nuna alamu ne na ciwon maƙoshi da kuma zazzaɓi a cibiyar lafiya ta makarantar a ranar 22 ga watan Fabrairu, inda kuma ya rasu a ranar 6 ga watan Maris.

A yanzu haka an fara gangamin yi wa mutane riga-kafi musamman yara da jam’ian kula da lafiya na makarantar, wanda hukumomi ke ganin za a faɗaɗa shi zuwa jihar baki-ɗaya.

Wata takardar gargaɗi kan lafiya ta buƙaci mazauna jihar su mayar da hankali kan tsafta da kuma guje wa shiga cunkoson mutane kuma su garzaya asibiti da zarar sun fara jin alamu irin na cutar diphtheria.

Kwamishinan lafiya na jihar Farfesa Akin Abayomi ya tabbatar wa da alumma cewa babu buƙatar su tayar da hankalinsu ganin cewa ana iya ƙoƙari wajen daƙile ɓarkewar cutar, kuma za a ci gaba da ɗaukar matakai domin kare su daga kamuwa da ita.

A shekarar 2023 ne aka samu ɓarkewar cutar diphtheria mafi girma a Najeriya inda ta yi sanadiyyar mutuwar mutane fiye da 600 akasari yara, kuma cutar ta shafi jihohi 19 cikin 36 da ke ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp