Home General Fubara ya rubutawa Majalisar Jihar Rivers Wasika

Fubara ya rubutawa Majalisar Jihar Rivers Wasika

Gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya sake rubuta wa majalisar dokokin jihar wasiƙar sanar da ƴanmajalisar aniyarsa ta sake gabatar da kasafin kuɗin jihar na shekarar 2025, domin neman amincewarsu.

Cikin wasiƙar da gwamnan ya aike wa kakakin majalisar dokokin jihar, Martin Amaewhule ranar Alhamis ya ce yana son gabatar da kasafin a gaban ƴanmajalisar a ranar Laraba 19 ga watan Maris, ko a wata rana cikin watan Maris da majalisar ke ganin zai fi dacewa.

Fubara ya ce matakin biyayya ce ga hukuncin Kotun Ƙolin ƙasar, da kuma buƙatar da ƴanmajalisar suka yi masa na sake gabatar musu kasafin kuɗin jihar.

A cikin wasiƙar gwamnan ya tuna wa kakakin majalisar zuwansa zauren majalisar a ranar Laraba da nufin gabatar da kasafin, amma sai aka kulle ƙofar aka hana shi shiga tare da tawagarsa.

“Za ka iya tuna ziyarar da kawo majalisar a ranar Laraba 12 ga watan Maris domin gabatar da kasafin, domin biyayya ga hukuncin Kotun Ƙoli, amma ba a ba ni damar shiga zauren majalisar ba”, kamar yadda wani ɓangare na wasiƙar ya nuna.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp