Home General ‘Yan bindiga sun yi wa wasu ƙauyuka biyar dirar mikiya a Kaduna

‘Yan bindiga sun yi wa wasu ƙauyuka biyar dirar mikiya a Kaduna

Rahotanni daga Najeriya na cewa ‘yan bindiga sun yiwa wasu kauyuka biyar da suka haɗa da Unguwan Tauka, Unguwan Lalle, Sannu da zuwa, Tsauni Dodo da Dandauka, dukkansu a karkashin karamar hukumar Kachia ta jihar Kaduna dirar mikiyan ranar Alhamis.

Wani shugaban al’ummar yankin wanda ya tabbatar wa Daily Trust ta wayar tarho faruwar lamarin, ya ce ‘yan bindigar sun kuma kai farmaki a wani yankin Fulani da ke ƙauyen Kubuwo, inda suka yi awon gaba da wasu matasa makiyaya guda uku.

Ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 6 na yamma, inda ‘yan bindigar ɗauke da makamai suka yi ta kai farmaki tare da tilasta wa mutanen kauyukan tserewa yayin da suka riƙa harbin kan mai uwa dawabi.

Ya ce ‘yan bindigar sun gudu ne daga farmakin da sojoji suka kai a dajin Kurutu-Azara, wanda ke kan iyaka da karamar hukumar Kagarko kuma suka yanke shawarar ƙaddamar da mummunan hari a kan al’ummar da abin ya shafa.

A cewarsa, ‘yan bindigar sun kona wata mota da babur guda a Unguwar Tauka a lokacin da sojojin suka dakile sace wasu mutanen kauyen a yankin.

Rundunar ‘yansandan yankin ta tabbatar da faruwar harin amma bata bayyana cewa ko harin ya yi sanadin rayuwa ko kuma jikkata ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp