Kungiyoyin kwadagon Najeriya NLC da TUC sun yi kakkausan Allah wadai da abin da suka bayyana a matsayin saba doka da shugaba Tinubu ya yi, wajen kafa dokar ta-baci da dakatar da gwamnan jihar Siminilayi Fubara, da mataimakiyarsa, da yan majalisar dokokin jihar Rivers.
Kungiyoyin sun ce matakin ya saba wa tanadin sashe na biyu, da sashe na 305 na kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 wanda aka yi wa kwaskwarima, kuma ya zama cin zarafi ga ikon zartarwa.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kungiyoyin suka fitar ranar Larabar nan,kwana guda bayan shugaba Tinubu ya sanar da matakin na sa, da ya haifar da ce-ce-ku-ce a fadin kasar.
Sanarwar ta bukaci shugaban kasar ya gaggauta janye sanarwar da ya bayar, da ka iya dora kasar a kan tubalin sabawa doka a nan gaba.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 18 hours 34 minutes 53 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 20 hours 16 minutes 18 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com