Home General NLC ta bukaci Tinubu ya gaggauta Mayar da Fubara

NLC ta bukaci Tinubu ya gaggauta Mayar da Fubara

Kungiyoyin kwadagon Najeriya NLC da TUC sun yi kakkausan Allah wadai da abin da suka bayyana a matsayin saba doka da shugaba Tinubu ya yi, wajen kafa dokar ta-baci da dakatar da gwamnan jihar Siminilayi Fubara, da mataimakiyarsa, da yan majalisar dokokin jihar Rivers.

Kungiyoyin sun ce matakin ya saba wa tanadin sashe na biyu, da sashe na 305 na kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 wanda aka yi wa kwaskwarima, kuma ya zama cin zarafi ga ikon zartarwa.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kungiyoyin suka fitar ranar Larabar nan,kwana guda bayan shugaba Tinubu ya sanar da matakin na sa, da ya haifar da ce-ce-ku-ce a fadin kasar.

Sanarwar ta bukaci shugaban kasar ya gaggauta janye sanarwar da ya bayar, da ka iya dora kasar a kan tubalin sabawa doka a nan gaba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp