Home General Dakatar da Fubara cin zarafin Demukradiyya ne – Gwamnonin PDP

Dakatar da Fubara cin zarafin Demukradiyya ne – Gwamnonin PDP

Gwamnonin jam’iyyar PDP sun buƙaci Shugaban Najeriya Bola Tinubu da ya janye dakatarwar da ya yi wa gwamnan Rivers Siminalayi Fubara.

Ƙungiyar Gwamnonin ta PDP ta bayyana dakatarwar da aka yi wa Fubara a matsayin “babban kuskure” sannan mummunan mataki ne da zai haifar da koma-baya.”

A ranar Talata da daddare ne Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan jihar Rivers sakamakon ƙiƙi-ƙaƙar siyasa da aka daɗe ana gani a jihar da ke kudu maso kudancin Najeriya.

Shugaban ya kuma dakatar da Fubara da mataimakinsa da ƴanmajalisar dokokin jihar tare kuma da naɗa Ibok-Ete Ibas, tsohon soji mai muƙamin vice-admiral, a matsayin wanda zai ja ragamar al’amuran jihar.

Cikin wata sanarwa ranar Laraba, Bala Mohammed wanda shi ne gwamnan jihar Bauchi kuma shugaban kungiyar gwamnonin PDP, ya ce ayyana dokar ta-ɓacin a Rivers abin damuwa ne kan makomar jihar.

Gwamna Bala Muhammad ya ce jan baki ya yi shiru da Tinubu ya yi kan rawar da Nyesom Wike, ministan Babban Birnin Tarayyar Najeriya, Abuja ke takawa a rikicin siyasar na Rivers kamar ba shi dama ce ya yi kiɗinsa kuma ya yi rawarsa.

Ya ce “Wike ya zama doka saboda yana yin abin da kake so. Yanzu mun sani. Wannan sam babu dattako, an nuna son kai da kuma rarraba kawuna,” in ji sanarwar.

Kungiyar gwamnonin ta PDP ta ce matakin ƙarara barazana ce ga dimokraɗiyyar Najeriya sannan zai ƙara rura wutar rikici a ƙasar tare da ƙara janyo rashin yarda da lalata tattalin arziki da kuma zaman lafiyar ƙasa baki ɗaya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp