Home General Dakatar da Fubara cin zarafin Demukradiyya ne – Gwamnonin PDP

Dakatar da Fubara cin zarafin Demukradiyya ne – Gwamnonin PDP

Gwamnonin jam’iyyar PDP sun buƙaci Shugaban Najeriya Bola Tinubu da ya janye dakatarwar da ya yi wa gwamnan Rivers Siminalayi Fubara.

Ƙungiyar Gwamnonin ta PDP ta bayyana dakatarwar da aka yi wa Fubara a matsayin “babban kuskure” sannan mummunan mataki ne da zai haifar da koma-baya.”

A ranar Talata da daddare ne Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan jihar Rivers sakamakon ƙiƙi-ƙaƙar siyasa da aka daɗe ana gani a jihar da ke kudu maso kudancin Najeriya.

Shugaban ya kuma dakatar da Fubara da mataimakinsa da ƴanmajalisar dokokin jihar tare kuma da naɗa Ibok-Ete Ibas, tsohon soji mai muƙamin vice-admiral, a matsayin wanda zai ja ragamar al’amuran jihar.

Cikin wata sanarwa ranar Laraba, Bala Mohammed wanda shi ne gwamnan jihar Bauchi kuma shugaban kungiyar gwamnonin PDP, ya ce ayyana dokar ta-ɓacin a Rivers abin damuwa ne kan makomar jihar.

Gwamna Bala Muhammad ya ce jan baki ya yi shiru da Tinubu ya yi kan rawar da Nyesom Wike, ministan Babban Birnin Tarayyar Najeriya, Abuja ke takawa a rikicin siyasar na Rivers kamar ba shi dama ce ya yi kiɗinsa kuma ya yi rawarsa.

Ya ce “Wike ya zama doka saboda yana yin abin da kake so. Yanzu mun sani. Wannan sam babu dattako, an nuna son kai da kuma rarraba kawuna,” in ji sanarwar.

Kungiyar gwamnonin ta PDP ta ce matakin ƙarara barazana ce ga dimokraɗiyyar Najeriya sannan zai ƙara rura wutar rikici a ƙasar tare da ƙara janyo rashin yarda da lalata tattalin arziki da kuma zaman lafiyar ƙasa baki ɗaya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp