Home General Gwamna Abba ya nada Aramposu mukami

Gwamna Abba ya nada Aramposu mukami

Gwamnan jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusif, ya yi sabbin naɗe-naɗe tare da ɗaga likkafar wasu mutane a ƙunshin gwamnatinsa.

Mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar a daren Laraba, inda ya ce canje-canjen zai ƙara gogar da shugabannin gobe masu tasowa da kuma ƙara inganta kyakkyawan jagorancin gwamnatin jihar.

Sabbin naɗe-naɗe sune kamar haka;

1- Akitek Hauwa Hassan Tudun Wada – shugabar hukumar kula da tsara birane ta jihar kano (KNUPDA)

2- Mustapha Muhammad – Sakataren yaɗa Labaran Gwamnan kuma mataimakin kakakin Gwamnan.

3- Auwal Lawan Aramposu – Mataimakin Shugaban hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta Kano (KAROTA).

4- Dakta Tukur Ɗaiyabu Minjibir – Mai bawa Gwamnan shawara kan harkokin Noma da Kiwo (Agriculture).

Haka kuma gwamnan ya amince da ɗaga likkafar wasu ƙusoshin gwamnatin guda biyu waɗanda suka haɗar da;

1- Hajiya Zulaihat Yusuf Aji – Mataimakiyar Shugaban gidan rediyon Kano, wanda a baya ta kasance babbar mai bawa Gwamna Shawara kan yaɗa labarai.

2- Injiniya Abduljabbar Nanono – Mataimakin Shugaban hukumar samar da wutar lantarki ta jihar kano KHEDCO, wanda a baya shine Mashawarcin Gwamnan akan sabbin dabarun makamashi.

A ƙarshe gwamnan ya taya su murnar muƙaman da suka samu, har ma ya buƙaci suyi aiki tuƙuru wajen sauke nauyin da aka ɗora musu domin samun nasarar gwamnatin na ciyar da jihar gaba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp