Home General Kotun koli ta tabbatar da Anyanwu a matsayin sakataren jam’iyyar PDP

Kotun koli ta tabbatar da Anyanwu a matsayin sakataren jam’iyyar PDP

Kotun Kolin Najeriya ta soke hukuncin da kotun ɗaukaka ƙara ta zartas a baya, na dakatar da na hannun damar Nyesom Wike Sanata Samuel Anyanwu, a matsayin sakataren jam’iyyar PDP na kasa.

A wani hukunci da alkalan kotun mutum biyar suka yanke da mai shari’a Jamilu Tukur ya gabatar, kotun Kolin ya soki kotun ɗaukaka ƙara da babban Kotun jihar Enugu na shiga abin da ta kira rikicin cikin gida.

Tun a baya babbar kotun da ke Enugu ta cire Anyanwu a matsayin sakataren jam’iyyar bisa ƙarar da wani ɗan jam’iyyar PDP Mista Aniagu Emmanuel ya shigar.

Hakazalika kotun ɗaukaka ƙara a jihar ta tabbatar da hukuncin babban kotun wanda ya amince da Cif Udeh-Okoye a matsayin wanda ya maye gurbin Sanata Anyanwu a matsayin sakataren Jam’iyya.

Bayan rashin amincewa da hukuncin, Anyanwu ya ɗaukaka ƙarar zuwa kotun ƙoli.

Anyanwu da Sunday Ude-Okoye sun soma rikici kan matsayin sakataren jam’iyyar ne tun bayan da Anyanwu ya bar matsayin domin yin takara a zaɓen gwamnan Imo wanda ya yi rashin nasara.

Bayan rashin nasararsa, ƙoƙarin dawowa kan kujerarsa ya jefa jam’iyyar cikin rikici wanda ya kawo rarrabuwar kai tsakanin ƴan ƙungiyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp