Home General Kotu ta ɗage shari’ar Nnamdi Kanu bayan cigaba da zama a yau...

Kotu ta ɗage shari’ar Nnamdi Kanu bayan cigaba da zama a yau Juma’a

Jagoran haramtacciyar ƙungiyar ‘yan’aware ta Indigenous People of Biafra (IPOB) ya sake bayyana a gaban babbar kotun tarayya yau Juma’a a Abuja babban birnin Najeriya.

Sai dai ɗaya daga cikin lauyoyinsa Aloy Ejimakor ya ce kotun ƙarƙashin Mai Shari’a James Kolawole ta ɗage cigaba da sauraron ƙarar zuwa 29 ga watan Afrilu da kuma 2 da 6 ga watan Mayu na 2025.

Ci gaba da shari’ar ta Nnamdi Kanu na zuwa ne bayan Alƙaliyar Alƙalai Kudirat Kekere-Ekunnyefere ta saka Mai Shari’a James Kolawole Omotoshi a matsayin sabon alƙalin da zai saurari shari’ar bayan Kanu ya yi ƙorafi kan Mai Shari’a Binta Nyako.

An yi hasashen za a yi bitar tuhuma bakwai da gwamatin Najeriya ke yi wa Kanu yayin ci gaba da shari’ar, waɗanda suka jiɓanci tayar da fitina da kuma ta’addanci.

A watan Disamban 2023 ne Kotun Ƙoli ta umarci Kanu ya koma babbar kotun ta tarayya domin kare tuhumar da ake yi masa bayan Binta Nyako ta yi watsi da takwas cikin 15 da gwamnati ta gabatar a 2021.

Gwamnatin Najeriya ta kai Kanu kotu ne bayan kama shi a wata ƙasar waje a 2021, kuma har yanzu mambobin ƙungiyarsa da gwamnati ta haramta na ci gaba da neman ɓallewa daga Najeiriya domin kafa ƙasar Biafra.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp