Home General M23 ta sake ƙwace wani yanki a Congo bayan watsi da kiran...

M23 ta sake ƙwace wani yanki a Congo bayan watsi da kiran tsagaita wuta

Shugaban ‘yan tawayen M23 da ke samun goyon bayan Rwanda a gabashin Congo ya yi watsi da tayin da Kinshasa da Kigali suka yi na tsagaita wuta cikin gaggawa, yayin da dakarunsa suka shiga cikin yankunan gabashin Congo tare da sake ƙwace garin Walikale mai muhimmanci.

Bayan karɓe ikon wasu manyan birane guda biyu a gabashin ƙasar ta Congo, birnin na Walikale dake da tazarar kilomita 125 daga babban birnin ƙasar Kinshasa wanda ke ɗaya daga cikin masu tarin arzikin ma’adanai da ya shiga kwamar ƴan tawayen na M23.

Garin mai yawan al’umma 15,000 ya faɗa ƙarƙashin ikon ƴan tawayen ne bayan wani ƙazamin faɗa da ya ɓarke a tsakaninsu da dakarun sojin ƙasar ta Jamhuriyyar Congo.

Faɗan, wanda ya samo asali daga kisan kiyashi da aka yi a kasar Rwanda a shekarar 1994 da kuma gogayya kan mallakar arzikin albarkatun ƙasa, shi ne mafi muni a gabashin Congo tun bayan yakin shekarar 1998 zuwa 2003 wanda ya yi sanadin mutuwar miliyoyin mutane.

A yayin da masana suka bayyana cewa wannan yaƙin da ƙasashen Congo da Rwanda da kuma Burundi suka tsunduma cikinsa a wannan shekara, ya munana bisa yadda yake ƙoƙarin bazuwa yankin baki ɗayansa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp