Home General Gwamna Abba ya nada Aramposu mukami

Gwamna Abba ya nada Aramposu mukami

Gwamnan jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusif, ya yi sabbin naɗe-naɗe tare da ɗaga likkafar wasu mutane a ƙunshin gwamnatinsa.

Mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar a daren Laraba, inda ya ce canje-canjen zai ƙara gogar da shugabannin gobe masu tasowa da kuma ƙara inganta kyakkyawan jagorancin gwamnatin jihar.

Sabbin naɗe-naɗe sune kamar haka;

1- Akitek Hauwa Hassan Tudun Wada – shugabar hukumar kula da tsara birane ta jihar kano (KNUPDA)

2- Mustapha Muhammad – Sakataren yaɗa Labaran Gwamnan kuma mataimakin kakakin Gwamnan.

3- Auwal Lawan Aramposu – Mataimakin Shugaban hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta Kano (KAROTA).

4- Dakta Tukur Ɗaiyabu Minjibir – Mai bawa Gwamnan shawara kan harkokin Noma da Kiwo (Agriculture).

Haka kuma gwamnan ya amince da ɗaga likkafar wasu ƙusoshin gwamnatin guda biyu waɗanda suka haɗar da;

1- Hajiya Zulaihat Yusuf Aji – Mataimakiyar Shugaban gidan rediyon Kano, wanda a baya ta kasance babbar mai bawa Gwamna Shawara kan yaɗa labarai.

2- Injiniya Abduljabbar Nanono – Mataimakin Shugaban hukumar samar da wutar lantarki ta jihar kano KHEDCO, wanda a baya shine Mashawarcin Gwamnan akan sabbin dabarun makamashi.

A ƙarshe gwamnan ya taya su murnar muƙaman da suka samu, har ma ya buƙaci suyi aiki tuƙuru wajen sauke nauyin da aka ɗora musu domin samun nasarar gwamnatin na ciyar da jihar gaba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp