Home General Gwamna Abba ya nada Aramposu mukami

Gwamna Abba ya nada Aramposu mukami

Gwamnan jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusif, ya yi sabbin naɗe-naɗe tare da ɗaga likkafar wasu mutane a ƙunshin gwamnatinsa.

Mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar a daren Laraba, inda ya ce canje-canjen zai ƙara gogar da shugabannin gobe masu tasowa da kuma ƙara inganta kyakkyawan jagorancin gwamnatin jihar.

Sabbin naɗe-naɗe sune kamar haka;

1- Akitek Hauwa Hassan Tudun Wada – shugabar hukumar kula da tsara birane ta jihar kano (KNUPDA)

2- Mustapha Muhammad – Sakataren yaɗa Labaran Gwamnan kuma mataimakin kakakin Gwamnan.

3- Auwal Lawan Aramposu – Mataimakin Shugaban hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta Kano (KAROTA).

4- Dakta Tukur Ɗaiyabu Minjibir – Mai bawa Gwamnan shawara kan harkokin Noma da Kiwo (Agriculture).

Haka kuma gwamnan ya amince da ɗaga likkafar wasu ƙusoshin gwamnatin guda biyu waɗanda suka haɗar da;

1- Hajiya Zulaihat Yusuf Aji – Mataimakiyar Shugaban gidan rediyon Kano, wanda a baya ta kasance babbar mai bawa Gwamna Shawara kan yaɗa labarai.

2- Injiniya Abduljabbar Nanono – Mataimakin Shugaban hukumar samar da wutar lantarki ta jihar kano KHEDCO, wanda a baya shine Mashawarcin Gwamnan akan sabbin dabarun makamashi.

A ƙarshe gwamnan ya taya su murnar muƙaman da suka samu, har ma ya buƙaci suyi aiki tuƙuru wajen sauke nauyin da aka ɗora musu domin samun nasarar gwamnatin na ciyar da jihar gaba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp