Dakatar da gwamnan Rivers bata sunan Najeriya ne a idon duniya – Jonathan

Tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya soki dakatar da gwamnan jihar Rivers da mataimakiyarsa da ƴanmajalisar dokokin jihar, wanda shugaban ƙasar, Bola Tinubu ya yi.

Jonathan ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi a matsayin shugaban taro wanda gidauniyar Haske Satumari ta shirya a ranar Asabar a Abuja, inda ya bayyana rashin jin daɗinsa kan matakin na cire zaɓaɓɓun shugabanni.

“Wannan matakin da aka ɗauki zai ɓata sunan Najeriya ne a idon duniya,” in ji shi, kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.

Jonathan ya ce duk da cewar akwai buƙatar ɗaukar matakan da za su magance rikicin siyasar da ya dabaibaye jihar Rivers na tsawon lokaci, a cewarsa dakatar da waɗanda mutane suka zaɓa a matsayin shugabanninsu bai dace ba.

Ya ƙara da cewa ya san bai kamata a matsayinsa tsohon shugaban ƙasa ya cika maganganu barkatai a game da abubuwan da suke a ƙasar ba, amma “yadda ake kallon Najeriya yana ta’allaƙa ne a kan matakan ɓangaren zartaswa da majalisa da na shari’a suka ɗauka,” in ji shi.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 18 hours 47 minutes 39 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 20 hours 29 minutes 4 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com