‘Yanbindiga sun kashe jami’an tsaro 10 a jihar Zamfara

‘Yanfashin daji sun kashe dakarun rundunar tsaro a jihar Zamfara 10 a wani kwanton ɓauna da suka yi musu ranar Asabar.

Gwamnan Zamfara Dauda Lawal ya ce shida daga ciki dakarun tsaron gwamnatin jihar ne da ake kira Askarawa, huɗu kuma ‘yan sa-kai ne.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, gwamnan ya ƙara da cewa akwai dakarun Asakarawa biyu da ɗan sa-kai ɗaya da suka ɓata.

“Lamarin ya faru ne bayan farmakin da gamayyar jami’an tsaro [ciki har da Askarawa] ƙarƙashin jagorancin sojojin Najeriya suka kai wa sansanin ‘yanbindiga a Dajin Sunƙe, wanda aka samu gagarumar nasarar kashe da dama tare da ƙwato makamai masu tarin yawa,” in ji Gwamna Lawal.

Ya ce tuni aka yi jana’izarsu a yau Lahadi, yana mai cewa ya bayar da umarnin ɗaukar “matakin bayar da agajin gaggawa ga waɗanda suka ji raunuka” da kuma “bayar da tallafin gaggawa ga iyalan waɗanda suka rasu”.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 14 hours 51 minutes 38 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 16 hours 33 minutes 3 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com