Home General ‘Ya Ta’adda sun kashe masallata 44 a Nijar

‘Ya Ta’adda sun kashe masallata 44 a Nijar

Hukumomi a Jamhuriyar Nijar sun ayyana makoki kwana uku bayan wasu ‘yanbindiga sun kashe aƙalla mutum 44 yayin da suke sallar Juma’a.

Rahotonni sun ce harin ya jikkata mutum 13, huɗu daga cikinsu na cikin mawuyacin hali a harin da aka kai garin Kokorou da ke kan iyakar Nijar da Mali da Burkina Faso.

Wata sanarwa da Ministan Harkokin Cikin Gida Mohamed Toumba ya fitar ta ce maharan da ke biyayya ga ƙungiyar Islamic State wato Islamic State in the Greater Sahara (ISGS) ne suka kai harin a ranar Asabar.

“Da misalin ƙarfe 2:00 na rana, daidai lokacin da Musulmai ke yin sallar Juma’a maharan suka kewaye masallacin domin aikata kashe-kashen da ba a saba gani ba,” in ji ministan.

Kazalika, sun cinna wa “kasuwa da gidajen mutane wuta,” kamar yadda ya bayyana.

Kwana biyu kafin wannan hari rundunar sojin Nijar ta ce ta kashe mambobin ISGS 45.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp