Home General ‘Ya Ta’adda sun kashe masallata 44 a Nijar

‘Ya Ta’adda sun kashe masallata 44 a Nijar

Hukumomi a Jamhuriyar Nijar sun ayyana makoki kwana uku bayan wasu ‘yanbindiga sun kashe aƙalla mutum 44 yayin da suke sallar Juma’a.

Rahotonni sun ce harin ya jikkata mutum 13, huɗu daga cikinsu na cikin mawuyacin hali a harin da aka kai garin Kokorou da ke kan iyakar Nijar da Mali da Burkina Faso.

Wata sanarwa da Ministan Harkokin Cikin Gida Mohamed Toumba ya fitar ta ce maharan da ke biyayya ga ƙungiyar Islamic State wato Islamic State in the Greater Sahara (ISGS) ne suka kai harin a ranar Asabar.

“Da misalin ƙarfe 2:00 na rana, daidai lokacin da Musulmai ke yin sallar Juma’a maharan suka kewaye masallacin domin aikata kashe-kashen da ba a saba gani ba,” in ji ministan.

Kazalika, sun cinna wa “kasuwa da gidajen mutane wuta,” kamar yadda ya bayyana.

Kwana biyu kafin wannan hari rundunar sojin Nijar ta ce ta kashe mambobin ISGS 45.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp