Home General Ba za mu yi haɗaka da kowa ba – SDP

Ba za mu yi haɗaka da kowa ba – SDP

Jam’iyyar SDP a Najeriya ta yi watsi da yunkurin haɗaka tsakaninta da sauran jam’iyyun adawa da nufin tunkarar zaɓen 2027.

Wannan na zuwa yayin da ake ganin tagomashin jam’iyyar ta SDP ya karu sakamakon sauya shekar da wasu manya ‘yansiyasa a kasar ke yi zuwa cikinta

A makon da ya gabata ne wasu jagororin adawa ƙarƙashin jagorancin tsohon mataimakin shugaban ƙasa Alhaji Atiku Abubakar na babbar jam’iyyar hamayya ta PDP suka sanar da cewa suna wani yunƙuri na ƙulla haɗaka domin kawar da APC a zaɓen 2027.

Sai dai shugaban jam’iyyar na kasa Alhaji Shehu Musa Gabam a hirarsa da BBC ya ce SDP ba za ta haɗe da wata jam’iyya ba.

“Mun faɗa wa duniya cewa mu ba za mu yi maja ba, ba maganan haɗewa domin akwai ƙa’idoji kuma rashin cika ƙa’idojin wata fitina ce,” in ji shi.

Ya ce babu hannun SDP a yunƙurin hadewar jam’iyyun adawa domin a cewarsa jam’iyarsu tana da tsari.

Shugaban SDP ya ce sai dai duk wanda yake son ya shigo ya zo don gina jam’iyyar.

Ya ce tsarinsu shi ne, duk wanda yake son shiga jam’iyyar zai tafi ne mazaɓarsa, daga nan zai iya takarar duk muƙamin da yake so.

Alhaji Shehu Musa Gabam ya bayyana shakku kan haɗakar jam’iyyu a Najeriya inda ya yi zargin yadda jam’iyya mai mulki ke shiga cikin jam’iyyun adawa tana karya su.

“Ba mu san su wane ne da kuma manufofin da za su shigo da su ba, wannan ya sa NWC ya ƙayyade cewa babu maganar maja,” in ji shugaban jam’iyyar SDP.

Ya ƙara da cewa tsarin jam’iyyarsu ya sha bamban da sauran jam’iyyu musamman batun korar ƴan jam’iyya da ake yi daga mazaɓar mutum.

Ya ce shugaban jam’iyya a mazaɓa ba ya da ikon korar mutum sai da amincewar shugabancin jam’iyyar.

Tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai na cikin manyan ƴansiyasar da suka sauya sheƙa zuwa SDP, wanda kuma a wata hira da BBC ya yi wa wasu manyan jagororin adawa tayin sabuwar jam’iyyar tasa.

Shugaban jam’iyyar SDP ya ce akwai ƴansiyasa sama da 200 da suka yi murabus daga jam’iyyunsu suka shigo SDP, sai dai bai bayyana sunayensu ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp