Home General Ba za mu yi haɗaka da kowa ba – SDP

Ba za mu yi haɗaka da kowa ba – SDP

Jam’iyyar SDP a Najeriya ta yi watsi da yunkurin haɗaka tsakaninta da sauran jam’iyyun adawa da nufin tunkarar zaɓen 2027.

Wannan na zuwa yayin da ake ganin tagomashin jam’iyyar ta SDP ya karu sakamakon sauya shekar da wasu manya ‘yansiyasa a kasar ke yi zuwa cikinta

A makon da ya gabata ne wasu jagororin adawa ƙarƙashin jagorancin tsohon mataimakin shugaban ƙasa Alhaji Atiku Abubakar na babbar jam’iyyar hamayya ta PDP suka sanar da cewa suna wani yunƙuri na ƙulla haɗaka domin kawar da APC a zaɓen 2027.

Sai dai shugaban jam’iyyar na kasa Alhaji Shehu Musa Gabam a hirarsa da BBC ya ce SDP ba za ta haɗe da wata jam’iyya ba.

“Mun faɗa wa duniya cewa mu ba za mu yi maja ba, ba maganan haɗewa domin akwai ƙa’idoji kuma rashin cika ƙa’idojin wata fitina ce,” in ji shi.

Ya ce babu hannun SDP a yunƙurin hadewar jam’iyyun adawa domin a cewarsa jam’iyarsu tana da tsari.

Shugaban SDP ya ce sai dai duk wanda yake son ya shigo ya zo don gina jam’iyyar.

Ya ce tsarinsu shi ne, duk wanda yake son shiga jam’iyyar zai tafi ne mazaɓarsa, daga nan zai iya takarar duk muƙamin da yake so.

Alhaji Shehu Musa Gabam ya bayyana shakku kan haɗakar jam’iyyu a Najeriya inda ya yi zargin yadda jam’iyya mai mulki ke shiga cikin jam’iyyun adawa tana karya su.

“Ba mu san su wane ne da kuma manufofin da za su shigo da su ba, wannan ya sa NWC ya ƙayyade cewa babu maganar maja,” in ji shugaban jam’iyyar SDP.

Ya ƙara da cewa tsarin jam’iyyarsu ya sha bamban da sauran jam’iyyu musamman batun korar ƴan jam’iyya da ake yi daga mazaɓar mutum.

Ya ce shugaban jam’iyya a mazaɓa ba ya da ikon korar mutum sai da amincewar shugabancin jam’iyyar.

Tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai na cikin manyan ƴansiyasar da suka sauya sheƙa zuwa SDP, wanda kuma a wata hira da BBC ya yi wa wasu manyan jagororin adawa tayin sabuwar jam’iyyar tasa.

Shugaban jam’iyyar SDP ya ce akwai ƴansiyasa sama da 200 da suka yi murabus daga jam’iyyunsu suka shigo SDP, sai dai bai bayyana sunayensu ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp