Har yanzu ba’a ga watan sallah a Nijeriya ba

Majalisar ƙoli ta harkokin addinin musulunci a Najeriya ƙarƙashin jagorancin mai alfarma Sarkin Musulmi Alh. Muhammad Sa’ad Abubakar ya bayyana cewa akwai yuwar a ci gaba da azumi a ranar Lahadi domin zuwa yanzu ba’a ga wata a Najeriya ba.

Majalisar ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da babban sakatareta Farfesa Ishaq Oloyede ya sanya wa hannu a yau Asabar.

“Idan Musulmai suka ga jinjirin wata bisa ga ka’idojin ganin watan, to mai alfarma zai bayyana ranar Lahadi 30 ga Maris, 2025 a matsayin 1 ga Shawwal da kuma ranar Idul Fitr.”

Idan daibzaku iya tunawa da yammacin wannan Rana hukumomi a kasar Saudiyya suka tabbatar da ganin jinjirin watar na karamar sallah Wanda ke bayyana ranar lahadi zasu gabatar da salla.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com