Home General An bayyana lokacin Janaídar Wamban Kano

An bayyana lokacin Janaídar Wamban Kano

Masarautar Kano ta yi rashin guda daga cikin manyan jagorin da su ka yi shura wurin al,amuran mulki da jagoranci shekaru masu tsawo, Galadiman Kano Alhaji Abbas Sanusi, dan sarkin Kano Abbas Abdullahi Bayero.

Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sanusi ya rasu ya na da shekaru 92 a duniya, a ranar talata da dare.

Ya kasance jigogin cikin wadanda da suka shahara a Masarautar Kano. A zamanin marigayi Sarkin Kano Alhaji Ado Bayero, shi ne Wamban Kano, Kuma Babban Dan majalisar Sarki.

Shugaban Jam’iyyar APC a jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas da Dan uwansa, Alhaji Kabiru Abbas su ne su ka tabbatar da rasuwar mahaifin na su bayan jinya da ya yi ta tsawon lokaci.

Rasuwar marigayi Galadiman Kano rashi ne ga al’ummar Arewacin Nijeriya ba ma iya masarautar kano ba kadai.

Ya rike mukamai daban-daban, karkashin Sarkin Kano Ado Bayero, wanda ya kasance a karagar masarautar daga shekarar 1963 zuwa 2014.

Ya rasu ya bar mata da ‘yaya 35, daga cikinsu akwai shugaban jami’iyyar APC na jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas.

Za a gudanar da jana’izarsa a  fadar masarautar Kano, dake kofar kudu da karfe 9 na safiyar ranar larabar nan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp