Home General Tinubu ya cire Mele Kyari daga shugabancin NNPCL

Tinubu ya cire Mele Kyari daga shugabancin NNPCL

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya cire Mele Kyari daga shugabancin kamfanin mai na ƙasar na NNPCL, inda ya maye gurbinsa da Injiniya Bashir Bayo Ojulari.

Wata sanarwa da mai magana da yawun shugaba Tinubun, Bayo Onanuga ya wallafa a shafinsa na X, ya ce hakan ya faru ne sakamakon wani garambawul da shugaban ya yi wa kamfanin.

Sanarwar ta ce shugaba Bola Tinubu ya rushe hukumar gudanarwar kamfanin ƙarƙashin shugabancin Cif Pius Akinyelure da kuma Mele Kyari wanda shi ne shugaban kamfanin.

“Shugaba Tinubu ya rushe dukkan mambobin hukumar da aka naɗa ƙarƙashin Pius Akinyelure da Mele Kyari a 2023.” In ji sanarwar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp