Home General An bayyana lokacin Janaídar Wamban Kano

An bayyana lokacin Janaídar Wamban Kano

Masarautar Kano ta yi rashin guda daga cikin manyan jagorin da su ka yi shura wurin al,amuran mulki da jagoranci shekaru masu tsawo, Galadiman Kano Alhaji Abbas Sanusi, dan sarkin Kano Abbas Abdullahi Bayero.

Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sanusi ya rasu ya na da shekaru 92 a duniya, a ranar talata da dare.

Ya kasance jigogin cikin wadanda da suka shahara a Masarautar Kano. A zamanin marigayi Sarkin Kano Alhaji Ado Bayero, shi ne Wamban Kano, Kuma Babban Dan majalisar Sarki.

Shugaban Jam’iyyar APC a jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas da Dan uwansa, Alhaji Kabiru Abbas su ne su ka tabbatar da rasuwar mahaifin na su bayan jinya da ya yi ta tsawon lokaci.

Rasuwar marigayi Galadiman Kano rashi ne ga al’ummar Arewacin Nijeriya ba ma iya masarautar kano ba kadai.

Ya rike mukamai daban-daban, karkashin Sarkin Kano Ado Bayero, wanda ya kasance a karagar masarautar daga shekarar 1963 zuwa 2014.

Ya rasu ya bar mata da ‘yaya 35, daga cikinsu akwai shugaban jami’iyyar APC na jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas.

Za a gudanar da jana’izarsa a  fadar masarautar Kano, dake kofar kudu da karfe 9 na safiyar ranar larabar nan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp