Home General Rasuwar Galadima: Gwamnan Kano ya mika ta’aziyyarsa ga shugaban APC Abdullahi Abbas

Rasuwar Galadima: Gwamnan Kano ya mika ta’aziyyarsa ga shugaban APC Abdullahi Abbas

Gwamnatin jihar Kano ta mika sakon ta’aziyya ga mai martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, Majalisar Masarautar Kano da kuma Shugaban Jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alh. Abdullahi Abbas da sauran iyalai, bisa rasuwar Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sanusi.

Marigayi Galadiman Kano, wanda ya rasu yana da shekaru 91 a daren ranar Talata a Kano, ya kasance fitaccen dattijo kuma jigo a masarautar Kano. Ya sadaukar da rayuwarsa wajen hidimtawa Masarautar, ya rike manyan mukaman sarauta da suka hada da Wamban Kano, ya kuma taka muhimmiyar rawa a Masarautar a karkashin marigayi Sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar Kano Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ya sanyawa hannu kuma raba manema labarai a jihar Kano.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana wannan rashin a matsayin babban rashin, ba wai ga Masarautar kadai ba har ma da jihar da daukacin al’ummar Kano baki daya

Gwamna Abba Kabiru ya yaba da kyawawan halaye na Marigayi Galadiman Kano, a matsayinsa na mutum mai kishi da jajircewa wajen kiyaye al’adun Kano.

Bugu da kari, gwamnan ya jajantawa daukacin al’ummar jihar Kano, bisa babban rashi na Alhaji Abbas Sanusi. Ya kuma yi addu’ar Allah ya jikansa da rahama ya kuma baiwa iyalansa hakurin jure wannan babban rashi.

Gwamna Yusuf ya bukaci al’ummar Kano da su rika sanya marigayi Galadiman Kano a cikin addu’o’insu don neman masakuma kiyaye kimar hadin kai da hidima da ya tsaya a kai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp