Home General Rasuwar Galadima: Gwamnan Kano ya mika ta’aziyyarsa ga shugaban APC Abdullahi Abbas

Rasuwar Galadima: Gwamnan Kano ya mika ta’aziyyarsa ga shugaban APC Abdullahi Abbas

Gwamnatin jihar Kano ta mika sakon ta’aziyya ga mai martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, Majalisar Masarautar Kano da kuma Shugaban Jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alh. Abdullahi Abbas da sauran iyalai, bisa rasuwar Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sanusi.

Marigayi Galadiman Kano, wanda ya rasu yana da shekaru 91 a daren ranar Talata a Kano, ya kasance fitaccen dattijo kuma jigo a masarautar Kano. Ya sadaukar da rayuwarsa wajen hidimtawa Masarautar, ya rike manyan mukaman sarauta da suka hada da Wamban Kano, ya kuma taka muhimmiyar rawa a Masarautar a karkashin marigayi Sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar Kano Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ya sanyawa hannu kuma raba manema labarai a jihar Kano.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana wannan rashin a matsayin babban rashin, ba wai ga Masarautar kadai ba har ma da jihar da daukacin al’ummar Kano baki daya

Gwamna Abba Kabiru ya yaba da kyawawan halaye na Marigayi Galadiman Kano, a matsayinsa na mutum mai kishi da jajircewa wajen kiyaye al’adun Kano.

Bugu da kari, gwamnan ya jajantawa daukacin al’ummar jihar Kano, bisa babban rashi na Alhaji Abbas Sanusi. Ya kuma yi addu’ar Allah ya jikansa da rahama ya kuma baiwa iyalansa hakurin jure wannan babban rashi.

Gwamna Yusuf ya bukaci al’ummar Kano da su rika sanya marigayi Galadiman Kano a cikin addu’o’insu don neman masakuma kiyaye kimar hadin kai da hidima da ya tsaya a kai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp