Home General Rasuwar Galadima: Gwamnan Kano ya mika ta’aziyyarsa ga shugaban APC Abdullahi Abbas

Rasuwar Galadima: Gwamnan Kano ya mika ta’aziyyarsa ga shugaban APC Abdullahi Abbas

Gwamnatin jihar Kano ta mika sakon ta’aziyya ga mai martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, Majalisar Masarautar Kano da kuma Shugaban Jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alh. Abdullahi Abbas da sauran iyalai, bisa rasuwar Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sanusi.

Marigayi Galadiman Kano, wanda ya rasu yana da shekaru 91 a daren ranar Talata a Kano, ya kasance fitaccen dattijo kuma jigo a masarautar Kano. Ya sadaukar da rayuwarsa wajen hidimtawa Masarautar, ya rike manyan mukaman sarauta da suka hada da Wamban Kano, ya kuma taka muhimmiyar rawa a Masarautar a karkashin marigayi Sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar Kano Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ya sanyawa hannu kuma raba manema labarai a jihar Kano.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana wannan rashin a matsayin babban rashin, ba wai ga Masarautar kadai ba har ma da jihar da daukacin al’ummar Kano baki daya

Gwamna Abba Kabiru ya yaba da kyawawan halaye na Marigayi Galadiman Kano, a matsayinsa na mutum mai kishi da jajircewa wajen kiyaye al’adun Kano.

Bugu da kari, gwamnan ya jajantawa daukacin al’ummar jihar Kano, bisa babban rashi na Alhaji Abbas Sanusi. Ya kuma yi addu’ar Allah ya jikansa da rahama ya kuma baiwa iyalansa hakurin jure wannan babban rashi.

Gwamna Yusuf ya bukaci al’ummar Kano da su rika sanya marigayi Galadiman Kano a cikin addu’o’insu don neman masakuma kiyaye kimar hadin kai da hidima da ya tsaya a kai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp