Rahotannin daga jihar Borno da ke arewa maso gabashin Nijeriya na bayyana cewa wasu da ake zargin mayakan Boko Haram ne sun kai hari sansanin horas da ‘yan sanda na PMFTC da ke Limankara, a Gwoza, inda suka kashe Sufeton ’yan sanda guda ɗaya.
Sun kai harin da misalin ƙarfe 6 na safiyar ranar Alhamis, 3 ga watan Afrilu, 2025, yayin da jami’an tsaro suka fita sintiri a ƙafa.
Read Also:
Sufeto Andrawus Musa daga rundunar 6PMF da ke Maiduguri ya samu rauni a harin, inda maharan suka ƙwace bindigarsa ƙirar AK-47.
An kai shi asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri (UMTH), amma rai ya yi halinsa.
Rundunar dai na gudanar da bincike kan harin, tare da ƙoƙarin ganin ta kama waɗanda suka kai hari.
Ta kuma nemi jama’a da suke sanya ido kan duk wani abun zargi, tare da bai wa jami’an tsaro rahoto.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1485 days 14 hours 24 minutes 34 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1467 days 16 hours 5 minutes 59 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021
Report By: PRNigeria.com